Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home KASUWANCI

Nijeriya Ke Da Yanayi Mafi Rudu A Duniya Kan Harkar Sufurin Jiragen Sama – Na’Allah

by Tayo Adelaja
September 26, 2017
in KASUWANCI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abubakar Abba, Kaduna

Mataimakin Shugaban masu rinjaye na Majalisar Dattawa, Sanata Bala Ibn Na’Allah ya koka akan irin yanayin da ake dashi a kasar nan ta harkar zirga-zirgar jiragen sama.

samndaads

Na’Allah wanda shine Mataimakin Shugaban Kwamiti na Majalisar Dattawa a harkar sufurin jiragen Sama.

Ya ce, “a ilmance, abin da nake nufi shine, mu ke da yanayi mafi rudarwa a duniya wajen gudanar da sufurin jiragen sama kuma harkar ba za ta iya ci gaba karkashin wannan yanayi.”

A cewar shi, wadanda suka zuba jari a harkar, da kyar suke samun riba, domin wani lokaci, ribar tana tafiya ne akan masu ruwa da tsaki, kamar matuki da kamfanin Inshora da Injiniyoyi da sauran ma’aikata da kuma masu sa ido akan tafiyar da harkar.

Sanata Na’Allah ya ci gaba da cewa, hukumomi masu sa ido akan harkar, sun dage sai lallai wadanda suka zuba jari a harkar sun biya da Dalar Amurka, alhali yawancinsu, basu da kudaden biyan.

Ya yi nuni da cewa, idan aka ci gaba da tafiya a hakan, harkar ta sufurin jiragen sama, ba za ta taba ci gaba ba a yanzu a kasar nan.

Ya bayyana cewa, masu sa ido a harkar sun zama wani karfen kafa,don sun ga sune keda wuka da nama akan lura da harkar.

Ya ce, bai kamata ba a rinka tsawwalawa masu yin harkar ta hanyar cazar su makudan Dalar Amurka.

Na’Allah ya bayyana cewa,Nijeriya tana daya daga cikin ‘ya’ya ta kungiyar  Sufurin jiragen sama ta kasa da kasa(ICAO), wadda ta baiwa matuka jirgin sama damar da suyi amfani da damar taron na garin Cape, wajen bayar da hayar jirage da tashin su.

A cewar shi, wannan yarjejenyar, a karkashin dokar Nijeriya, an amince da ita, kuma za ta taimakawa matukan jiragen.

Ya ce, a saboda hakan wadanda suka bada hayar jiragen su a karkashin yarjejeniyar ta garin Cape, tasa su dole suka dawo da jiragen su gida.

A karshe Sanatan ya koka akan yadda ganin mafi yawanci dalibai matuka jiragen sama da aka yaye a kasar nan wadanda basu samu aikn yi ba.

SendShareTweetShare
Previous Post

A Shekarar 1974, Hukumar IMF Na Zuwa Nijeriya Neman Rance

Next Post

Wani Kamfanin Chana Zai Gina Masakar Da Ba Irinta A Nijeriya

RelatedPosts

Sugar

Alakar Dake Tsakanin Sukari Ca Ciwon Suga

by Muhammad
3 weeks ago
0

Da yawa a yankin kasashen nahiyar Afirka ana ganin sukari...

A Na Cigaba Da Zaman Doya Da Man Ja Tsakanin Majalisa Da Shugaba Trump

Ba Da Mugun Nufi Shugaba Buhari Ya Garkame Iyakoki Ba – Ministar Kudi

by Abdulaziz Kabir Muhammad
1 year ago
0

Ministar kudi da tsaretsare, Uwargida Zainab Ahmed Shamsuna, ta sanar...

Gwamnatin Tarraya Ta Kebe Biliyan N2.6 Don Aikin Tashar Mambilla A 2020

by Abdulaziz Kabir Muhammad
1 year ago
0

Sama da shekaru arba’in da suka shude kenan da bada...

Next Post

Wani Kamfanin Chana Zai Gina Masakar Da Ba Irinta A Nijeriya

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version