Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji

byAbubakar Abba
2 months ago
Nijeriya

A kowace shekara, Nijeriya na tafka asarar dala biliyan biyu, kwatankwacin Naira tiriliyan 3.2, sakamakon watsi da yin nona a Gandun Dazukan ƙasar.

Wasu ƙwararru a fannin aikin noma ne suka bayyana hakan, inda suka sanar da cewa; idan da ana gudanar da ayyukan noma a Gandun Dazukan ƙasar, za a iya ƙara bunƙasa tattalin arziƙin kasuwanci na ƙasar.

Kazalika, sun yi nuni da cewa; idan da ana amfani da Gandun Dazukan wajen yin noma, da za a iya ƙara faɗaɗa harkar kusuwancin noma.

Har ila yau, sun ƙara da cewa; hakan kuma zai sanya a ƙara samar da ayyukan yi a tsakanin mata da matasa, ta yadda ƙananan manona da ƙananan masu sarrafa amfanin gona a ƙasar za su ɗauke su, su riƙa yi musu aiki.

Shugaban ƙungiyar manoma don samun riba na ƙasa, Ibrahim Kabiru ya bayyana cewa; ta hanyar yin shuke-shuken kamar kayan marmari da suka haɗa da bishiyoyin Mangoro, Lemon zaƙi, Gwaiba, Kwakwar Manja da sauran makamantansu a Gandun Dazukan ƙasar, Nijeriya za ta iya samun kuɗaɗen shiga da yawansu ya kai kimanin dala biliyan biyu, daidai da Naira tiriliyan 3.2.

  • Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana
  • Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Zama Sakatariyar Kungiyar Yaƙi Da Cutar Daji

“Ta hanyar gudanar da ɗimbin ayyukan noma a Gandun Dazukan wannan ƙasa, zai yi matuƙar ƙara yawan ayyukan masana’antun ƙasar da ke sarrafa amfanin gona domin fitarwa zuwa kasuwannin duniya, don sayarwa”, in ji Ibrahim.

Kazalika, Ibrahim wanda kuma shi ne shugaban ƙungiyar manoma ta ƙasa (AFAN) ya jaddada cewa; idan aka samu goyon bayan ma’aikatar aikin noma da samar da wadataccen abinci da kuma goyon bayan sauran hukumomin, hakan zai bayar da damar gyara Gandun Dazukan da ake da su, musamman wajen kare su daga kwararowar hamada.

Shugaban ya ƙara da cewa, akasarin noman gargajiya a ƙasar nan, ana yin sa ne a karkara, inda manoma a karkara ke shuka ‘ya’yan itatuwa na kayan marmari a Gandun Dazukan ƙasar.

Ya ci gaba da cewa, mazauna karkara na yin amfani da Gandun Dazukan ƙasar wajen yin kiwon dabbobi, wanda hakan ke ƙara bunƙasa ayyuka a tsakanin mazauna karkarar.

Shugaban ya yi nuni da cewa, gudanar da ayyukan noma a Gandun Dazukan wannan ƙasa, zai yi matuƙar kawo ci gaba ga Nijeriya tare da samar da ɗauki ga marasa ƙarfi, wanda kuma hakan zai bai wa mata da matasa damar jawo su a jiki, domin tafiya tare da su.

A cewarsa, har yanzu ba a makara ba, domin kuwa za a iya yin amfani da Gandun Dazukan ƙasar wajen gudanar da ayyukan noma.

Shugaban ya ci gaba da cewa, hakan zai ƙara taimaka wa a samar da wadataccen abinci a ƙasar da kare kwararowar hamada da kuma annobar sauyin yanayi.

Ya bayyana cewa, za a iya cimma hakan ne kaɗai idan mahukunta a ƙasar suka samar da kyakywan tsari tare da gangamin wayar da kan jama’a da kuma zuba hannun jari

a fannin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Next Post
Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

LABARAI MASU NASABA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version