Nijeriya Na Bukatar Karin Basuka – Ministan Kudi
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Bukatar Karin Basuka – Ministan Kudi

byKhalid Idris Doya
10 months ago
Nijeriya

Ministan kudi da tsare-tsaren tattalin arziki, Wale Edun, ya ce, gwamnatin tarayya tana bukatar karin wasu basukan kudade domin ta cike gibin kasafin kudinta, duk kuwa da cewa wasu ma’aikatu da rassa da sashi-sashi sun inganta harsashen hanyoyin shigar kudinsu.

Ministan ya shaida hakan ne yayin ganawa da hadakar kwamitin majalisar dattawa na kudin da na tsare-tsaren harkokin tattalin arziki kan tsarin kashe kudade na 2025 zuwa 2027.

  • Dikko Radda Ya Bai Wa Gwarazan Hikayata Kyautar Kudi
  • Karancin Takardar Kudi: Masu POS Da Bankuna Na Wasa Da Hankulan Jama’a

Edun ya ce akwai bukatar cikin basukan muddin majalisar dattawa ta amince da hakan.

“Yunkurin da ake yi kan kudin shiga yana tafiya daidai, amma akwai bukatar a kara himma, muna bukatar karin basuka masu albarka, inganci da dourewa.

“Ba kawai don gine-gine da manyan ayyukan ba, har ma don ayyukan jin dadi da walwalar jama’a, ayyukan kiwon lafiya, ilimi da ayyuka a fannonin kiyaye tsaron jama’a don taimaka wa masu karamin karfi da masu fama da talauci,” Edun ya shaida.

A nasa bangaren, ministan kasafi da tsare-tsaren tattalin arziki, Sanata Atiku Bagudu ya tunatar da ‘yan majalisar yunkurin ciwo bashi tiriliyan 35.5 a kasafin 2024, da farko an yi nufin sanar da gibin tiriliyan 9.7.

“Duk da tsare-tsaren kudaden shiga ya zarta na wasu hukumomin samar da kudaden shiga, har yanzu akwai bukatar gwamnati ta karbo rancen kudade don gudanar da kasafin kudin yadda ya kamata, musamman ta fuskar rabe-rabe da samar da ayyukan yi ga marasa galihu.

“Muna da tsarin hangen nesa na ci gaba na dogon lokaci na 2050,” in ji Bagudu.

Kazalika, shugaban hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC), Ola Olukoyede, ya shaida wa kwamitin cewa hukumarsa ta kwato sama da naira biliyan 197 daga watan Janairun 2024,

Ya lura cewa idan gwamnati ta yi aiki tukuru kuma ta samu tarin abubuwan da ake bukata, kasar za ta samu isassun kudaden da za ta kashe a kasafin kudin.

Babban Kwanturolan Hukumar Kwastam ta Nijeriya, Bashir Adeniyi, a cikin jawabinsa, ya bayyana cewa hukumar ta kwastam ta tara naira tiriliyan 5.352 na kudaden shiga fiye da naira tiriliyan 5.09 da aka yi niyyar yi a kasafin kudin shekarar 2024.

Ya ci gaba da cewa, naira tiriliyan 6.3 an yi niyya ne a matsayin kudaden shiga da aka yi hasashen za a samu a shekarar 2025, wanda kasha 10 daga ciki zai kasance abin da ake sa ran samun kudaden shiga a shekarar 2026 da karin kashi 10 na kasafin kudin shekarar 2027.

A nasa jawabin, babban jami’in gudanarwa na rukunin kamfanin man fetur na Nijeriya (NNPCL), Mele Kyari, ya ce kamfanin ya zarce kudaden shiga na naira tiriliyan 12.3 da aka yi hasashen za a iya samu a shekarar 2024, inda ya riga ya tara naira tiriliyan 13.1.

Har ila yau, shugaban hukumar tara haraji ta kasa FIRS, Zacch Adedeji, a nasa jawabin, ya sanar da kwamitocin hadin gwiwa cewa FIRS ta zarce kudaden shiga da aka yi niyya a sassa daban-daban na haraji.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

October 3, 2025
Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho
Tattalin Arziki

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

October 3, 2025
Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG
Tattalin Arziki

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

September 27, 2025
Next Post
Kidayar Jama’a Da Harkar Lafiya

Kidayar Jama'a Da Harkar Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version