Nijeriya Ta Nanatawa Amurka Kudirinta Na Ci Gaba Baiwa 'Yan Jarida 'Yanci
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Nanatawa Amurka Kudirinta Na Ci Gaba Baiwa ‘Yan Jarida ‘Yanci

bySulaiman
2 years ago
Amurka

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ƙara tabbatar wa da gwamnatin Amurka cewa Nijeriya na kan turbarta na tabbatar da ‘yancin ‘yan jarida da kafafen yaɗa labarai.

Ya ce, akwai buƙatar wannan ‘yanci sosai domin ta hanyar kafafen yaɗa labarai ne dimokuraɗiyya ke ƙara karsashi, tasiri da nagarta a cikin zukatan al’umma.

  • Minista Ya Biya Tarar Naira Miliyan 585 Domin A Saki Daurarru 4,068
  • Manufar Sin Ta Baiwa Kasashe Damar Shigowa Kasarta Ba Tare Da Biza Ba Za Ta Bunkasa Mu’amala Tsakanin Jama’a Da Jama’a

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwar da mataimaki na musamman a fannin yaɗa labarai ga ministan, Malam Rabi’u Ibrahim, ya fitar a ƙarshen mako.

Ministan ya bayyana haka a lokacin da Babban Jami’in Amurka mai Kula da Al’amurran Nijeriya, Mista David Greene, ya kai masa ziyara a ofishinsa.

Ya ce: “A yayin da mu ke goyon baya da tabbatar da ‘yancin kafafen yaɗa labarai da na ‘yan jarida, mu na kuma yin kira ga gwamnatin Amurka da ta ba mu goyon baya ta hanyar ƙara zurfafa horaswa ga ‘yan jarida, musamman a fannin binciken tabbatar da gaskiya da fayyace sahihin labari daga labaran bogi.”

Idris ya ƙara da cewa, “Yin hakan zai ƙara rage yawan watsa labaran bogi, bayanan karkatar da hankalin jama’a, da rage bazuwar ji-ta-ji-ta acikin al’umma.”

Ministan ya jaddada aniyar da Nijeriya ta sa a gaba wajen ƙara wa dimokuraɗiyya daraja da ƙima, ya na mai cewa, “Muhimmin abu ne a matsayin Amurka na babbar ƙawar Nijeriya ta ƙara zurfafa goyon bayanta ga gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, a ƙoƙarin da gwamnatin ke yi na bunƙasa tattalin arzikin ƙasar.”

A jawabin sa, Mista Greene ya ce Amurka na goyon bayan Nijeriya ɗari bisa ɗari wajen inganta dimokuraɗiyya da inganta ayyukan kafafen yaɗa labarai.

Ya ce an keto shekaru da dama ƙasarsa ta na bayar da guraben ƙaro ilmi, bada horaswa da kuma fannin inganta tsaro.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Next Post
Yakin Zirin Gaza: An Kara Kwanaki Biyu Na Tsagaita Bude Wuta

Yakin Zirin Gaza: An Kara Kwanaki Biyu Na Tsagaita Bude Wuta

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version