Nijeriya Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Aikin Hajjin 2024
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Aikin Hajjin 2024

byYusuf Shuaibu
2 years ago
nahcon

Gwamnatin tarayyar Nijeriya da Kasar Saudiyya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar gudanar da aikin hajjin 2024 a Jedda.

Ministan harkokin waje, Yusuf Tuggar shi ne ya jagoranci tawagar Nijeriya, yayin da ministan gudanar da aikin Hajji da Umara, Dakta Taufik Al-Rabiah ya jagoranci tawagar Saudiyya.

  • Shari’ar Kano: Kanawa Na Farin Ciki Kan Nasarar Abba A Kotun Koli
  • Shiriya, Ni’ima Da Gaskiyar Manzon Allah (SAW)

Mataimakiyar daraktan harkokin hukumar aikin hajjin Nijeriya, (NAHCON), Fatima Usara ta bayyana cewa tawagar ‘yan Nijeriya da suka halarci taron rattaba hannun ciki har da mukaddashin shugaban hukumar NAHCON, Jalal Arabi, sun bukaci karin wa’adi ga masu jigilar ‘yan Nijeriya tare da neman a kawo karshen matsalar da aka samu a lokacin hajjin bara a Mina.

Haka kuma gwamnatin tarayya ta bukaci ministan aikin hajji da umara na Kasar Saudiyya da ya ziyarci Nijeriya.

A nasa bangaren, Rabiah ya amince da kalubalen da aka samu a aikin hajjin bara a Mina, sannan ya bayar da tabbacin cewa ana kokarin inganta amfani da murabba’in fili mita miliyan 2 ga maniyyata miliyan biyu domin gudanar da aikin hajj a duk shekara.

Da yake amsa goron gayyatan zuwa Nijeriya nan ba da jimawa ba, Rabiah ya bayyana goyon bayan ma’aikatar wajen daukar matakan da suka dace na bai wa alhazai yanayi mai kyau domin gudanar da aikin hajji cikin natsuwa.

Haka kuma ya jaddada wa tawagar hukumar NAHCON sabon tsarin da aka fito da shi a harabar Masha’ir.

Dangane da bukatar da NAHCON ta shigar na samar da isasshen fili a Mina, Rabiah ya bayyana muhimmancin ajiye kudade da wuri domin samun wuraren da ya dace a Masha’ar, inda ya ce hakan ya sa ma’aikatarsa ta sabunta tsarin wanda ya riga zuwa shi za a fara la’akari da shi.

Ya bukaci NAHCON ta yi kokarin cin gajiyar wannan sabon tsari domin samun wuri a Masha’ir, kamar Kasar Saudiyya take kokarin guda da adalci wajen samun wuri.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Next Post
Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Goyi Bayan Kasashen Yammacin Afirka Da Na Sahel

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version