Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

byAbba Ibrahim Wada
4 days ago
Nijeriya

A hankali dai tawagar ‘yanwasan kwallon kafa ta kasa Super Eagles tana sake samun kwarin gwiwar damar zuwa gasar cin kofin duniya sakamakon hukunce-hukuncen da hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA take yi a kan wasu kasashen da suka aikata laifi a lokacin buga wasannin neman cancantar shiga gasar.

Kwamitin ladabtarwa na hukumar kwallon kafa FIFA ya sanar matakin da ta dauka a kan tawagar kwallon Afirka ta Kudu, inda ta rage mata maki uku, sannan ta ci ta tarar kudi.

  • Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
  • Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

Kwamitin ya gano kasar ta yi laifi ne wajen amfani da danwasan da bai kamata ya buga wasan ba, wanda tawagar da fafata da kasar Lesotho wato Teboho Mokoena da aka buga a ranar 21 ga watan Maris na shekarar 2025.

FIFA ta ce amfani da danwasan ya saba da sashe na 19 da kundin laifuka na hukumar, sannan ya kuma saba da sashe na 14 na kundin shirye-shiryen farko-farko na gasar cin kofin duniya na shekarar 2026.

FIFA ta ce bayan nazarin binciken da aka gudanar, ta kwace nasarar da Afirka ta Kudu ta samu, sannan ta ba kasar Lesotho nasara a wasan. Wadanda aka ladabtar saboda laifukan dai suna da kwana 10 domin daukaka kara a gaban kwamitin daukaka kara na kwamitin ladabtarwa na Hukumar FIFA.

 

Me Hakan Ke Nufi Ga Tawagar Nijeriya?

Ga Yadda Tsayuwar Rukunin C Yake

A ranar 9 ga watan Satumba ne tawagar Super Eagles ta Nijeriya ta tashi da kunnen doki a wasan da ta buga da tawagar ta Afirka ta Kudu a wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya. Bayan wasan ne kasar Afirka ta Kudu ta kara zama a saman teburi da maki 17 cikin wasa takwas da ta buga a Rukunin C.

Tawagar Jamhuriyar Benin ke biye mata da maki 14, sai kuma Nijeriya da ke mataki na 3 da maki 11.

Sai dai kuma Nijeriya ta kasance tana da maki daya ne da na Rwanda da ke mataki na 4, sai kuma kasar Lesotho da ke da maki 6 a mataki na 5, sai kuma Zimbabwe ta karshe da maki 4.

Kasashe tara ko 10 ne za su wakilci nahiyar Afirka a gasar cin kofin duniya na 2026, wadda kasashe 48 za su fafata kuma kasashen Amurka da Medico da Canada za su karbi bakunci.

 

Canjin Da aka samu Bayan Hukunci

A ka’idar wasannin neman gurbin, duk tawagar da ta kare a mataki na daya daga kowane rukuni guda tara na nahiyar Afirka ce za ta samu gurbi kai-tsaye. Daga baya sai a zabo hudu mafiya kokari da suka kare a mataki na 2, inda za a fitar da daya daga cikinsu sannan ta kara da wata tawagar daga nahiyar.

Yanzu da aka rage wa Afirka ta Kudu maki uku, zai zama tana da maki 14 kenan, dai-dai da tawagar kasar Benin, ita kuma kasar Lesotho ta samu karin maki uku zuwa maki tara maimakon shida a baya kafin a kara mata maki uku.

Yanzu wasa biyu ne suka rage wa kowace tawaga, inda Nijeriya take bukatar samun nasara a wasannin guda biyu. Idan ta samu nasara a wasannin da za ta buga da Lesotho da Benin, zai zama Nijeriya da maki 17 ke nan jimilla.

Sai dai kuma hakan zai ta’allaka ne da wasannin sauran kungiyoyin, domin idan Afirka ta Kudu ko Benin daya daga ciki ta ci wasa daya, ta yi canjaras a wasa daya, za ta koma maki 18. Amma idan ta yi rashin nasara a wasa daya, ta ci daya za ta tsaya da maki 17 ne, daidai ke nan da idan Nijeriya ta samu nasara a wasanninta biyu na gaba.

Ita Benin yanzu damarta ta karu, kuma akwai wasa tsakanin Nijeriya da Benin, wasan da za a iya kira da raba gardama domin shi ne wasan Nijeriya na karshe a rukunin na C.

Ke nan Nijeriya ta fi bukatar samun nasara a wasanninta biyu na gaba, sannan Afirka ta Kudu da Benin su rasa wasanninsu biyu na gaba, inda za ta kara da maki 17, su kuma suna 14. Haka kuma idan Nijeriya da Afirka ta Kudu suka karkare da maki daya, Super Eagles na bukatar kwallaye fiye da Afirka ta Kudu haka ita ma Benin. Yanzu haka Afirka ta Kudu na da yawan kwallaye +8, yayin da Nijeriya ke da +2.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane
Wasanni

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni
Wasanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar
Wasanni

Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar

October 6, 2025
Next Post
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

LABARAI MASU NASABA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version