Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Yi Kuskure A Wasanta Na Farko –Okocha

by
4 years ago
in WASANNI
2 min read
Nijeriya Ta Yi Kuskure A  Wasanta Na Farko –Okocha
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Labarai Masu Nasaba

Chiellini Ya Bar Juventus

Wasan Damben Cin Mota: An Fara Fafatawa A Kano

‘Yan Nijeriya na ci gaba da tofa albarkacin bakinsu akan rashin nasarar da tawagar kwallon kafar kasar ta Super Eagles ta yi, a wasan farko da ta buga na gasar cin kofin duniya tsakaninta da Croatia.
Mafi akasarin magoya bayan ‘yan wasan na Super Eagles sun nuna rashin gamsuwa da kamun ludayin Nijeriya a wasan da ta yi rashin nasarar da 0-2.
Tsohon gwarzon dan wasan Super Eagles Jay Jay Okocha, na daga cikin wadanda suka yi tsokaci kan wasan na ranar Asabar,inda ya dora alhakin kayen da Nijeriya ta sha akan rashin dabara a bangaren mai horarwa da kuma ‘yan wasan.
Okocha, wanda ya bayyana haka yayin zantawarsa da gidan talabijin na Super Sports, ya ce ‘yan wasan Nijeriya sun buga wasan ne a guraben da basu saba buga wasa ba, lamarin da ya sa suka gaza nuna bajintarsu.
Tsohon dan wasan na Super Eagles ya bayar da misalin cewa kama ta yayi, kaftin din tawagar Super Eagles Mikel Obi, ya buga bangaren dan tsakiya mai tsaron gida, kamar yadda ya ke yi a lokacin da yake kungiyar Chelsea, amma ba sashin dan tsakiya mai jefa kwallo ba.
Okocha ya kara da cewa Aled Iwobi, wanda a halin yanzu shi ne mafi kwarewar dan wasan tsakiya a tsakanin ‘yan wasan na Super Eagles, kamata ya yi a wasan na ranar Asabar, ya buga bangaren tsakiyar, amma ba gefe ba.
A ranar 22 ga watan Yuni da muke ciki Nijeriya za ta fafata da Iceland, yayinda kuma a ranar 26 ga watan za ta buga da Argentina.
Laifin Mai Koyarwa Ne Ya Sa Mu Ka Yi Rashin Nasara, Cewar Ighalo
Dan wasan gaba na Nijeriya, Odion Ighalo, ya ce bai ji dadin yadda ya buga wasan da suka fafata da kasar Croatia ba, inda ya zama shi kadai ne tilo mai jefa kwallo na tawagar Super Eagles din.
Ighalo ya bayyana haka ne, yayin da yake sukar tsarin rarraba ‘yan wasa da mai horar dasu Gernot Rohr ya zaba, na sanya ‘yan wasa uku a baya, biyu a gabansu, uku a tsakiya sai kuma jefa kwallo daya a gaba, wato 3-2-3-1, sabanin tsarin da aka saba gani na hudu a baya, hudu a tsakiya, da kuma masu jefa kwallo biyu a gaba; 4-4-2.
Korafin na Ighalo na zuwa ne bayanda tsohon gwarzon dan wasan Nijeriya Jay Jay Okocha ya dora alhakin kayen da Nijeriya ta sha akan rashin dabara.
Okocha, ya ce mai horar da ‘yan wasan Nijeriyar ya sauya musu guraben da suka saba buga wasanni a kai, dalilin da ya hanasu tabuka wani abin azo a gani.
Tsohon dan wasan na Super Eagles ya bayar da misalin cewa kama ta yayi, kaftin din tawagar Super Eagles Mikel Obi, ya buga bangaren dan tsakiya mai tsaron gida, kamar yadda ya ke yi a lokacin da yake kungiyar Chelsea, amma ba sashin dan tsakiya mai jefa kwallo ba.
A ranar 22 ga watan Yuni da muke ciki Nijeriya za ta fafata da Iceland, yayinda kuma a ranar 26 ga watan za ta buga da Argentina.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Duk Da Haka Za Mu Fito Daga Cikin Rukuni –Jamus

Next Post

Bale Zai Ci Gaba Da Zama A Real Madrid Saboda Kociyan Kungiyar Ya Iya Turanci

Labarai Masu Nasaba

Chiellini

Chiellini Ya Bar Juventus

by Abba Ibrahim Wada
10 hours ago
0

...

dambe

Wasan Damben Cin Mota: An Fara Fafatawa A Kano

by Abba Ibrahim Wada
1 week ago
0

...

klopp

Har Yanzu Ban Hakura Da Lashe Firimiya Ba, Cewar Klopp

by Abba Ibrahim Wada
1 week ago
0

...

barcelona

Barcelona Ta Sa Hukumar La Liga Asarar Makudan Kudade

by Abba Ibrahim Wada
1 week ago
0

...

Next Post

Bale Zai Ci Gaba Da Zama A Real Madrid Saboda Kociyan Kungiyar Ya Iya Turanci

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: