Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Za Ta Buga Wasa A Legas Karon Farko Bayan Shekara 20

by
1 year ago
in WASANNI
2 min read
Tawagar ‘Yan Wasan Nijeriya Ta Kai Zagaye Na Biyu A Kofin Duniya
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Labarai Masu Nasaba

Chiellini Ya Bar Juventus

Wasan Damben Cin Mota: An Fara Fafatawa A Kano

Jihar Legas za ta karbi bakuncin wasan tawagar kwallon kafa ta Najeriya a karon farko tun bayan shekara 20 kamar yadda hukumar kula da wasannin kwallon kafa ta kasa ta bayyana wa manema labarai a ranar Litinin..

Super Eagles za ta kara da tawagar ‘yan wasan kasar Lesotho ranar 30 ga watan Maris a wasan neman shiga gasar cin kofin nahiyar Afirka da za su yi a filin wasa na Teslim Balogun dake jihar ta Legas.
Hukumar kwallon kafa ta Najeriya, NFF ta ce yawan mutanen da za su kalli karawar ya ta’allaka kan matakan hana yada cutar korona da hukumar kwallon kafa ta Afirka, CAF da za fitar kafin lokacin fafata wasan.
Wasa na karshe da Super Eagles ta buga a Legas shi ne a watan Janairun shekara ta 2001 wanda ta doke kasar Zambia a fafatawar shiga gasar cin kofin nahiyar Afirka kuma tun daga wancan lokacin ba’a sake kai wasan Nigeriya jihar Legas ba.
Sai dai a shekarar 2011, Najeriya ta buga wasan sada zumunta da tawagar kasar Saliyo, inda ta yi nasara a filin wasa na Teslim Balogun a jihar ta Legas da ci 1-0 wasan daya dauki ‘yan kallo masu yawa.
Ministan wasanni na Najeriya, Sunday Dare ya ce filin wasa na Legas zai ci gaba da karbar bakuncin wasannin kasar da zarar an kammala gyaran katafaren filin saboda haka nan gaba za’a dinga yawan kai wasa jihar.
Super Eagles ta ci gaba da yin wasanninta a wasu jihhohin fadin kasar, bayan da hukumar kwallon kafar Najeriya wato NFF kan tuntubi wadda keda sha’awar karbar bakuncin wasannin na kasa.
Duk jihar da ta karbi bakuncin Super Eagles kan taimaka da kudi wajen gudanar da wasannin kamar yadda ta buga a birnin Port Harcourt da Kano da Cross Riber da Akwa Ibom da Delta da kuma babban birnin tarayya Abuja.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Muna Fuskantar Manyan kalubale, Inji Shugaban Kungiyar Masu Kiwon Kaji

Next Post

Wasu Daga Cikin ’Yan Wasan Liverpool Sun Warke

Labarai Masu Nasaba

Chiellini

Chiellini Ya Bar Juventus

by Abba Ibrahim Wada
8 hours ago
0

...

dambe

Wasan Damben Cin Mota: An Fara Fafatawa A Kano

by Abba Ibrahim Wada
1 week ago
0

...

klopp

Har Yanzu Ban Hakura Da Lashe Firimiya Ba, Cewar Klopp

by Abba Ibrahim Wada
1 week ago
0

...

barcelona

Barcelona Ta Sa Hukumar La Liga Asarar Makudan Kudade

by Abba Ibrahim Wada
1 week ago
0

...

Next Post
'Yan Wasan Liverpool

Wasu Daga Cikin ’Yan Wasan Liverpool Sun Warke

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: