NIS: ACG James Sunday Ya Kai Ziyarar Inganta Aiki Maiduguri
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS: ACG James Sunday Ya Kai Ziyarar Inganta Aiki Maiduguri

bySadiq
2 years ago
NIS

Mataimakin Kwanturola Janar na Hukumar Shige da Fice ta Kasa (NIS), ACG James Sunday, ya ziyarci kwamandan rundunar Operation Hadin Kai a hedikwatar hukumar da ke Arewa maso Gabas a Maiduguri a karkashin jagorancin Manjo Janar W Shaibu domin tattauna gudunmawar da hukumar za ta bai wa rundunar a Maiduguri.

Taron ya samu halartar Babban Kwanturolan hukumar reshen Jihar Borno, CIS Abba Salihu da mataimakansa da ke shiyyar C, Manjo Janar W Shaibu da sauran manyan hafsoshin soji da ke hadin gwiwa da rundunar.

  • Kannywood Wuri Ne Na Nishadi Ba Gyaran Tarbiyya Ba -Fauziyya D Suleiman
  • Abubuwan Da Za Su Taimaka Wa Mai Azumi Ya Kasance Cikin Koshin Lafiya

Ko’odinetan Shiyyar C (Arewa maso Gabas), wadda ta kunshi jihohin Adamawa, Bauchi, Borno, Gombe, Yobe da Filato bayan sun ziyarci jihar Yobe, ya ziyarce su ne domin tantance ayyukan rundunar tare da jadadda umarnin sake bude iyakar Nijeriya da Jamhuriyar Nijar, sannan zai dawo Maiduguri domin ci gaba da ziyarar aikin kwanaki biyu a jihohin Borno da Yobe.

Haka zalika hukumar ta umarci rundundar da ke Jihar Borno da ta sake bude iyakar Nijeriya ci gaba da zirga-zirgar mutane zuwa Nijeriya da da sauran al’amuran yau da kullum kamar da yadda aka saba a baya.

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa tana da jami’ai da maza kusan 230 da aka tura zuwa rundunar hadin gwiwa, domin kyautata dangantakar ta aiki da hadin kai.

A cewar Kwamandan, jami’an NIS sun kware sosai wajen aikinsu dangane da shige da fice da sauransu. Jami’an sun samu horo da tsarin aiki karkashin jagorancin Manjo Janar W Shaibu kamar yadda aka bayyana a yayin taron.

“Ni da kaina na taso daga Maiduguri zuwa Damaturu domin tantance yanayin aikin da ake yi”, in ji ACG James.

“Ina tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa an samu kwanciyar hankali da tsaro a yankin Arewa maso Gabas, harkokin tattalin arziki da na cikin gida sun dawo a jihohin Barno da Yobe, motoci suna zirga-zirga cikin lafiya tare da kayayyaki zuwa sassan kasar nan.

“Ina mika godiya ga dukkan jami’an da ke kan hanyar da sojoji ke aiki ba dare ba rana a kewayen tafkin Chadi da kan iyaka, wannan namijin kokari ne kuma abun a yaba ne, in ji shi.

“Ina son jinjina wa jami’ain NIS tare da mika godiyata a gare su.”

Gwamnatin Jihar Borno ta za ta shirya wani babban taron tsaro a Maiduguri, bisa tsarin NIS a yankin Arewa Maso Gabas, don samar da hanyoyin da za a tabbatar da tsaro da zaman lafiya a yankin a kamar yadda mataimakin gwamnan jihar, Umar Usman Kadafur ya bayyana a lokacin da ya ziyarci ofishin hukumar na shiyyar C, da ke gidan gwamnatin jihar a Maiduguri.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Next Post
Wasannin Afirka 2024: Ko Ghana Za Ta Iya Abin Arziki?

Wasannin Afirka 2024: Ko Ghana Za Ta Iya Abin Arziki?

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version