Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

NIS Ta Cafke ‘Yan Mata Biyu Masu Amfani Da Fasfo Na Shigar Burtu

by Muhammad
January 22, 2021
in LABARAI
2 min read
Fasfo
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abdulrazak Yahuza Jere,

Jami’an Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS) da ke aiki a Filin Jiragen Sama na Murtala Mohammed da ke Legas sun damke wasu ‘yan mata biyu yayin da suke kokarin shiga jirgin Kamfanin Jiragen Sama na Egypt zuwa Kairo, ta hanyar amfani da fasfuna biyu da aka yi shigar burtu da su.

An gano su ne bayan Na’urar Tantance Bayanan Fasinjoji (MIDAS) ta ki tantance fasfunan da suka zo da su saboda bad da kama da aka masu game da asalin masu fasfunan.

Bayan an titsiye su lokacin bincike, sun ce za su yi balaguro ne na kasuwanci ta hanyar wani wakilinsu da suka kira da “Muri” wanda aka yi ta kiran lambar wayarsa ba ya amsawa. Ana zargin shi ne ya samar musu da fasfunan na shigar burtu masu dauke da hoton namiji a bayansu kamar yadda Na’urar MIDAS ta nuna. Wannan abin da Muri ya yi babban laifi ne idan har ya tabbata shi ya yi wanda zai fuskanci hukunci a karkashin dokokin shige da fice na 2015.

CGI Babandede dai ya sake gargadi ga wadanda suke amfani da fasfon Nijeriya su daina yin sakaci miyagu suna fakar idanunsu su sace musu fasfo domin aikata miyagun laifuka wanda idan aka kama mutum da yi zai fuskanci hukuncin dauri a gidan yari ko cin tara.

‘Yan matan biyu dai na taimakon jami’an hukumar ta NIS da muhimman bayanai da za su taimaka a cafke Muri don hukunta shi, kamar yadda sanarwar da ta fito daga jami’in yada labarun NIS, DCI Sunday James ta bayyana.

SendShareTweetShare
Previous Post

Yadda Muke Samun Rufin Asiri Ta Sana’ar Gadagi – Muhammadu Auwal  

Next Post

Za A Fadada Amfani Da Gas Na Girki Zuwa Yankunan Karkara A Nijeriya – Kyari  

RelatedPosts

An Yi Wa Buhari Da Osinbajo Allurar Rigakafin Korona

An Yi Wa Buhari Da Osinbajo Allurar Rigakafin Korona

by Sulaiman Ibrahim
1 hour ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim An yi wa Shugaba Muhammadu Buhari da...

Mukabalar

Kotu Ta Dakatar Da Yin Mukabalar Sheikh Abduljabbar Da Malaman Kano.

by Muhammad
7 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Wata kotu a Jihar Kano ta...

Ma'adanai

Masu Hakar Ma’adinai Ba Su Da Alaka a‘Yan Ta’adda -Shugaba

by Muhammad
7 hours ago
0

Daga Idris Aliyu Daudawa, Shugaban kungiyar masu hakar ma'adinai ta  Nijeriya...

Next Post
Gas

Za A Fadada Amfani Da Gas Na Girki Zuwa Yankunan Karkara A Nijeriya – Kyari  

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version