Abdulrazaq Yahuza Jere">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

NIS Ta Kaddamar Da Sansanin Karfafa Tsaron Iyakar Kasa Na 15 A Jihar Ogun

by Abdulrazaq Yahuza Jere
January 23, 2021
in LABARAI
2 min read
NIS Ta Kaddamar Da Sansanin Karfafa Tsaron Iyakar Kasa Na 15 A Jihar Ogun
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

A kokarinta na tabbatar da tsaron iyakokin kasar nan, Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS) ta kaddamar da sansanin jami’anta na kan-iyaka a garin Ilase da ke Jihar Ogun wanda ya zama cikon na 15 a cikin jerin wadanda ta kaddamar a sassa daban-daban na kasar nan.

Shugaban NIS, CGI Muhammad Babandede ya kaddamar da sansanin a ranar Juma’a 22 ga Janairun 2021. Sansanin dai wani bangare ne na kwarya-kwaryar gyaran fuska da sauye-sauye da hukumar ta NIS take aiwatarwa a sashen kula da iyakokin kasa domin sauke nauyin da kasa da ta dora mata.

samndaads

A jawabinsa yayin kaddamarwar, Babandede ya sake nanata kudirin shugabancinsa wajen tabbatar da cewa an samar da ire-iren wadannan sansanonin a dukkan iyakokin kasar nan domin karfafa sintiri na tsaro da kuma aiwatar da kyawawan manufofin da aka bullo da su na kula da iyakokin kasa kamar yadda ya kamata.

Ya bayyana cewa irin wannan sansanin zai kara kaimin yaki da bakin-haure wadanda ake fasa-kwaurinsu zuwa cikin kasa, da masu fataucin bil’adama da sauran miyagun laifukan da ake aikatawa a tsakanin iyakokin kasa da kasa.

Wakazalika, hukumar ta ce, kamar dai sauran sansanoni 14 da NIS ta riga ta kakkafa, shi ma sansanin na Ilase an kawata shi da kayan aiki na zamani da suka hada da na’urorin sadarwa da kayan more rayuwa domin jami’an hukumar su ji dadin sauke nauyin da aka dora musu na sintiri da sanya ido kan shige da ficen kasa a kan iyakoki.

 

 

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Sakataren Lamurran Sirri Na Gwamnan Bauchi Ya Yi Murabus

Next Post

Hadin Gwiwar Sin Da Afrika Kan Yaki Da COVID-19 Na Kara Fadada

RelatedPosts

Hadiza Usman

Hadiza Bala Usman Ta Yi Ta’aziya Ga Iyalan Marigayi Dikko Inde

by Abdulrazaq Yahuza Jere
3 hours ago
0

Daga Abdullahi Sheme A ranar juma'ar da ta gabatane shugabar...

Masana Sun Yaba Wa Shugaba Buhari Kan Sake Nada Hadiza Bala Usman Shugabar NPA

Masana Sun Yaba Wa Shugaba Buhari Kan Sake Nada Hadiza Bala Usman Shugabar NPA

by Abdulrazaq Yahuza Jere
3 hours ago
0

Daga Bello Hamza, Abuja Masana da masu ruwa da tsaki...

An Sako Daliban Da Aka Sace A Zamfara

An Sako Daliban Da Aka Sace A Zamfara

by Abdulrazaq Yahuza Jere
4 hours ago
0

Rahotanni daga jihar Zamfara sun tabbatar da cewa an ceto...

Next Post
Hadin Gwiwar Sin Da Afrika Kan Yaki Da COVID-19 Na Kara Fadada

Hadin Gwiwar Sin Da Afrika Kan Yaki Da COVID-19 Na Kara Fadada

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version