Abdulrazak Yahuza Jere">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

NIS Ta Karbi Karin Na’urorin Kula Da Shige Da Fice 63 Daga Kanada

by Abdulrazak Yahuza Jere
December 4, 2020
in LABARAI
2 min read
NIS
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

A wani bangare na hadin gwiwar da suka yi domin tabbatar da kula da shige da ficen jama’a a iyakokin kasa a zamanance, Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS) ta karbi karin gudunmawar na’urar tantance bayanan jama’a masu shige da ficen kasa daga Gwanatin Kasar Kanada.

Na’urorin dai ana aiki da su ne wajen tantance irin mutanen da suke shiga ko fita daga kasa a kan iyakoki.

samndaads

Da yake jawabi a yayin karbar na’urorin a Babban Filin Jiragen Sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja, ranar 4 ga Disambar 2020, shugaban NIS, CGI Muhammad Babandede, ya tabbatar da cewa ana fara amfani da na’urar; hukumar ta samu gagarumin ci gaba ta fuskar aikin tantance fasinjoji masu shiga ko fita daga kasa cikin kankanen lokaci.

Ya kara da cewa, zuwa yanzu, an sanya na’urorin a muhimman wurare daban-daban da suka hada da iyakokin kasa na filayen jiragen sama da na kan-tudu kuma wadannan sababbin da Gwamnatin Kanada ta bayar ta hannun Hukumar Kula da Shige da Fice ta Duniya (IOM) guda 63, za a yi amfani da su kamar yadda ya dace.

Sanarwar da jami’in hulda da jama’a na NIS, DCI Sunday James ya fitar a madadin shugaban hukumar, ta ce NIS ta rungumi amfani da na’urar ce domin bunkasa ayyukan kula da shige da ficen kasa tare da taimakon Kungiyar Tarayyar Turai da Kasar Japan da Jamus da Suwizilan da Danmak da kuma Nowai.

Sanarwar ta kara da cewa, a shekarar 2018 an kakkafa na’urar a manyan filayen jiragen saman kasar nan guda biyar da kuma wasu muhimman mashigan kasa.

SendShareTweetShare
Previous Post

Kasar Sin Na Kokarin Ganin An Raba Alluran Rigakafin COVID-19 Cikin Adalci

Next Post

Zan Raba Tallafi Ga Matan Karkara A Ko’ina – Minista Sadiya

RelatedPosts

Gobara Ta Kona Kasuwar Sakkwato

Gobara Ta Kona Kasuwar Sakkwato

by Abdulrazak Yahuza Jere
3 mins ago
0

Tambuwal Ya Kafa Kwamitin Bincike   Daga, Sharfaddeen Sidi Umar,...

A duniyar Nijeriya ta yanzu, da yawan mutane da ma masu lura da al’amuran yau da kullum su na kallon gudanar da zabukan kananan hukumomi

Abubuwan Al’ajabi A Zaben Kananan Hukumomin Kano

by Abdulrazak Yahuza Jere
10 hours ago
0

Kuri’un Da Aka Kidaya Sun Haura Na Zaben Gwamna A...

Ranar Bude Makarantu

Korona: Har Yanzu Babu Ranar Bude Makarantu A Jihar Kaduna

by Abdulrazak Yahuza Jere
10 hours ago
0

 Dukkanin makarantun Firamare da na sakandari da suke jihar Kaduna...

Next Post
Zan Raba Tallafi Ga Matan Karkara A Ko’ina – Minista Sadiya

Zan Raba Tallafi Ga Matan Karkara A Ko'ina - Minista Sadiya

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version