Abdulrazaq Yahuza Jere">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

NIS Ta Warware Mishkila A Kan Batun Fasfo Da Katin Dan Kasa

by Abdulrazaq Yahuza Jere
January 9, 2021
in LABARAI
2 min read
NIS Ta Warware Mishkila A Kan Batun Fasfo Da Katin Dan Kasa

Shugaban NIS Muhammad Babandede

WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa, CGI Muhammad Babandede ya sake nanata cewa wajibi ne duk wani mai neman sabon ingantaccen fasfo da hukumar ke bayarwa ya gabatar da lambar katin shaidar dan kasa.

A cewar Babandede, hakan ya zama tilas ne domin samun nasarar hade bayanan fasfo da na katin shaidar dan kasa wanda Hukumar NIMC ke bayarwa.

samndaads

Sanarwar da ta fito daga hukumar ta NIS ta hannun Jami’in hulda da jama’a, DCI Sunday James, ta bayyana cewa bisa la’akari da wajibcin katin dan kasar wajen yin fasfo da kuma yajin aikin da ma’aikatan hukumar samar da shaidar dan kasar (NIMC) ke yi, Hukumar Shige da Fice tana fayyace cewa, an samar da cibiyoyin NIMC a wasu sassa na NIS ne saboda saukaka hada-hadar kasuwanci a kasa domin masu yin fasfo kurum ta yadda ba sai sun sha wahala ba wajen neman inda ake yin katin dan kasar ba.

Sannan bayar da katin shaidar dan kasa ba shi daga cikin hurumin NIS. Don haka duk kudaden da ake biya na samun katin dan kasa, ko na sauya bayanan katin ko wani kudi na daban da ya shafin katin ba shi da alaka da NIS, saboda haka hukumar ba ta ci nanin ba, nanin ba zai ci ta ba.

Bugu da kari, sanarwar ta umurci kai rahoton duk wani jami’in NIS da yake cajar kudi mara ka’ida a kan NIN ko fasfo ta hanyar kiran lambobin waya kamar haka: 07080607900; 0814199908; ko shafin intanet: nis.servicom@nig.immigration.org.ng.

NIS ta kuma ce shugabanta CGI Babandede ya kafa wata tawaga ta musamman da za ta rika sanya ido domin tabbatar da ana samun nasarar aiki a dukkan ofisoshinta.

“Don haka, ana kira ga dukkan masu neman fasfo su biya kudi ta shafin intanet domin kauce wa fadawa hannun bata-gari, sannan NIS tana kara jaddada wa al’umma kudirinta na cimma bukatunsu a kan kari,” in ji sanarwar.

 

 

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Ranar Mazan Jiya 2021: Za Mu Ci Gaba Da Tuna Sojojin Da Suka Kwanta Dama -Buhari

Next Post

Jirgin Sama Dauke Da Fasinja 62 Ya Yi Batan-dabo A Indonesiya

RelatedPosts

Misali Daga Kebbi: Yadda Kananan Hukumomi Suka Shiga Uku A Nijeriya

Misali Daga Kebbi: Yadda Kananan Hukumomi Suka Shiga Uku A Nijeriya

by Abdulrazaq Yahuza Jere
2 hours ago
0

Kamar dai yadda aka sani kananan hukumomi sune suka kasance...

Abubuwan Da Suka Biyo Bayan Canja Shugabannin Tsaron Nijeriya

’Yan Yankin Arewa Maso Gabas Sun Bayyana Ra’ayoyinsu Kan Sauke Shugabannin Tsaro

by Abdulrazaq Yahuza Jere
2 hours ago
0

Biyo bayan sauke shugabannin tsaron Nijeriya tare da nada sababbi...

Ya Kashe Mata Da Yaro Da Shebur

by Abdulrazaq Yahuza Jere
2 hours ago
0

A yau aka kama wani mutum mai shekaru 28, Chukwuemeka...

Next Post
Jirgin Sama Dauke Da Fasinja 62 Ya Yi Batan-dabo A Indonesiya

Jirgin Sama Dauke Da Fasinja 62 Ya Yi Batan-dabo A Indonesiya

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version