Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Yaye Jami’anta 456 Da Aka Daga Darajarsu Karo Na Biyu

by
3 years ago
in LABARAI
2 min read
NIS Ta Yaye Jami’anta 456 Da Aka Daga Darajarsu Karo Na Biyu
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Labarai Masu Nasaba

Zargin Sauyin Sheka Yasa Majalisar Dokokin Kano Ta Dage Zamanta Na Ranar Litinin

Deborah: Kungiyar Gwamnonin Arewa Ta Bukaci A Zauna Lafiya

Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta kasa, Muhammad Babandede MFR ya jagoranci manyan baki da sauran jama’a wajen shaida faretin yaye jami’an shige da fice da aka daga darajar zuwa manyan jami’ai, karo na biyu da aka gudanar a Makarantar Horas da Jami’an NIS da ke Kano.
Bikin yaye jami’an dai ya samu halartar shugabannin sojoji, sauran rundunonin jami’an tsaro da hukumomin kai dauki, da wakilan masarautu da bangarorin addini da kuma mazumuntan hukumar ta NIS da ke Birnin Kano.
Da yake gabatar da jawabi a wajen, Muhammad Babandede ya karfafa gwiwar jami’an da aka daga darajar tasu su nuna shauki kan sabbin mukaman nasu na sufiritanda, ta hanyar dukufa ka-in-da-na-in ga aiki da kuma kauce wa duk wani abu da ka iya zubar da kima da martabar hukumarsu ta NIS, tare da zama jakadun hukumar nagari a duk inda suke.
A yayin da yake bayyana cewa sahun wadanda aka yayen a wannan matsayin a jiya Asabar su ne suka fara cin gajiyar Sabon Kundin Horaswa na NIS da aka koyar da su da shi, Babandede ya kuma gargadesu game da zuwa kamun kafa a turasu aiki a wurare masu maiko.
Shi ma da yake jawabi, Babban Kwamandan Makarantar Horaswar ta NIS da ke Kano, CIS Isma’il Hamis, ya gode wa shugaban hukumar bisa goyon bayan da yake bai wa makarantar da kuma namijin kokarinsa kan tabbatar da jami’an NIS suna samun horo a-kai-a-kai.
Haka nan ya bukaci jami’an da aka yayen su saka karamcin da aka yi musu na horas da su wajen bunkasa aikin hukumar a duk inda aka turasu aiki. Ya kuma jinjina wa takwarorin Hukumar NIS bisa hadin gwiwar da suke yi na aiki cikin zumunci da mutunci tun daga lokacin da ya kama aiki a matsayin Kwamandan makarantar ta Kano
Sanarwar da Shugaban na NIS Muhammad Babandede ya fitar ga manema labarai ta hannun jami’in yada labarun hukumar, Sunday James, ta yi tsokaci kan bikin yaye jami’an na NIS da aka daga darajarsu karo na biyu, inda ta ce abin ya yi armashi kuma ya kayatar sosai.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Sin Na Da Kwarewar Cimma Muradun Bunkasawar Tattalin Arziki A Manyan Fannoni

Next Post

An Kafa Cibiya Don Tunawa Da Dakta Yusufu Bala Usman

Labarai Masu Nasaba

Zargin Sauyin Sheka Yasa Majalisar Dokokin Kano Ta Dage Zamanta Na Ranar Litinin

Zargin Sauyin Sheka Yasa Majalisar Dokokin Kano Ta Dage Zamanta Na Ranar Litinin

by
13 hours ago
0

...

Deborah: Kungiyar Gwamnonin Arewa Ta Bukaci A Zauna Lafiya

Deborah: Kungiyar Gwamnonin Arewa Ta Bukaci A Zauna Lafiya

by
16 hours ago
0

...

Ganduje Ya Umurci Bala Ya Kula Da Ofishin Shugaban Ma’aikata Fadar Gwamnatin Kano

Ganduje Ya Umurci Bala Ya Kula Da Ofishin Shugaban Ma’aikata Fadar Gwamnatin Kano

by
21 hours ago
0

...

Deborah: Matasan Musulmai Ba Su Kona Min Gidana Ba —Bishop Kukah

Deborah: Matasan Musulmai Ba Su Kona Min Gidana Ba —Bishop Kukah

by Abubakar Abba
23 hours ago
0

...

Next Post

An Kafa Cibiya Don Tunawa Da Dakta Yusufu Bala Usman

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
 

Loading Comments...
 

    %d bloggers like this: