NIS Ta Yi Kawance Da NAPTIP Da IOM Domin Horas Da Jami’anta
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Yi Kawance Da NAPTIP Da IOM Domin Horas Da Jami’anta

byAbdulrazaq Yahuza
3 years ago
NIS

Hukumar Kula Da Shige Da Fice ta Kasa (NIS) ta yi kawance da takwararta ta duniya (IOM), da Hukumar Yaki Da Safarar Bil’adama (NAPTIP) da Sashen Ayyyukan Lafiya na PHS, wajen shirya wani taron kara wa juna sani da nufin samar da horo da dabarun aiki ga jami’anta.

An shirya horaswar ce a karkashin shirin da aka yi wa sunan TSI a takaice.

  • Yadda Ango Ya Yi Shahada Wajen Kare Amaryarsa Daga ‘Yan Bindiga

A wata sanarwa da Jami’in hulda da jama’a na NIS, Amos Okpu ya fitar, NIS ta bayyana cewa shirin yana samun tallafin hukumar kula da shige da fice ta duniya (IOM) da nufin bunkasa ayyuka a iyakokin kasa da kara sanya ido kan harkokin shige da fice a Nijeriya tare da taimaka wa hukumomin kula da shige da fice.

Shirin na da manufar bunkasa kwazo da hazakar jami’an da ke aiki a hukumomin dakile safarar mutane da shige da fice ta barauniyar hanya domin ayyuka su rika tafiya yadda ya dace a kowane lokaci.

NIS

Da yake jawabi a wajen kaddamar da shirin karo na na biyu, Shugaban Hukumar ta NIS, Isah Jere Idris, wanda ya samu wakilcin mataimakin kwanturola Janar mai kula da harkokin biza, Ishaka Abdulmumini Haliru, ya misalta kokarin abokan hukumar wajen kara bunkasa kwazon aikin jami’an NIS da NAPTIP a matsayin wani gagarumin ci gaba da zai kyautata harkokin shige da fice da dakile yawan safarar mutane ta barauniyar hanya, yana mai cewa hakan zai kara kyautata alaka a tsakanin bangarorin.

Ya ce, a kowani lokaci suna kula sosai da ba da fifiko ga sashin horar da jami’ansu domin tabbatar da ayyuka na gudana yadda ya dace, kan haka ne ma ya nuna farin cikinsa da wannan shirin.

NIS

A nata jawabin, darakta-janar ta Hukumar NAPTIP, Dakta Fatima Waziri-Azir, ta ce, IOM na tallafa wa shirye-shiryen da ke inganta kwazon jami’ai a fagen aiki a-kai-a-kai.

Ta yi kira ga hukumomi da jami’an da abin ya shafa da su yi amfani da wannan damar tallafin da suke samu daga kungiyoyin kasashen waje wajen inganta ayyukansu a kowani lokaci.

Sannan, ta bukaci jami’an NIS da NAPTIP da su ci gaba da kyautata alakar aiki mai inganci a tsakaninsu domin hada karfi da karfe waje guda don yaki da safarar mutane da jigila ta kai-komo ta barauniyar hanya.

Shi kuma a bangarensa, daraktan ayyukan lafiya na PHS, Dakta Geoffrey Okatubo, ya ce a ‘yan kwanakin baya sashen kula da lafiya ya fuskanci barazanar annobar korona da aka fuskanta, a yanzu kuma ga cutar kyandar biri (Monkey pox) da ake fama da ita a halin yanzu.

Sai ya nuna kwarin guiwarsa na cewa da hadin guiwar abokan aiki na cikin kasar Nijeriya da kasashen waje ana samun sakamako mai kyau wajen kula da lafiya.

NIS

Shugaban NIS, Isah Idris Jere ya sha nanata cewa zai mayar da hankali ga horas da jami’a domin inganta ayyukan hukumar a kowane sashe.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Next Post
Kwamitin tantance ‘Yan Takarar Shugaban Kasa Na APC Ya Yi Watsi Da ‘Yan Takara 10 Cikin 23

Kwamitin tantance 'Yan Takarar Shugaban Kasa Na APC Ya Yi Watsi Da 'Yan Takara 10 Cikin 23

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version