NIS Za Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Bayar Da Sabon Ingantaccen Fasfo A Zariya Da Daura
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Za Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Bayar Da Sabon Ingantaccen Fasfo A Zariya Da Daura

...Yayin Da Ganduje Ya Kaddamar Da Katafariyar Cibiyar Wallafa Fasfo A Kano

bySabo Ahmad
3 years ago
NIS

A kokarin da take yi na inganta ayyukan samar da fasfo ga dimbin masu nema da ke zaune a Kano da kewaye, Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS) ta kaddamar da Katafariyar Cibiyar Samar da Fasfo da za ta rika aiki ga ofisoshin fasfo na Jigawa, Katsina da kuma Dawakin Kudu da ke Kanon.

Da yake kaddamar da katafariyar cibiyar a ranar Laraba 11 ga Janairun 2023, Gwamna Abdullahi Umar na Jihar Kano ya taya NIS murna bisa dimbin nasarorin da take samu musamman kasancewarta ta farko da ta fara samar da sabon ingantaccen fasfo na zamani a duk fadin yankin Afirka.

Gwamnan wanda Kwamishinan Kasafin Kudi, Alhaji Danazumi Grazo ya wakilta ya jinjina wa NIS bisa kafa cibiyar a cikin Kano mai dimbin tarihi, yana mai cewa, ya yi amanna, zabar Kano da aka yi wajen kafa cibiyar ba zai rasa nasaba da yanayin zaman lafiya da ake mora a jihar ba.

A jawabinsa, Babban Shugaban NIS, Isah Jere Idris, MFR, ya tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa, ana samun ci gaba a shirin sauya fasalin fasfo da ake yi a halin yanzu, musannam kan tsarin yadda za a yi saurin gane waɗanda suka shigo daga sassa daban-daban na duniya.

Shugaban ya ce, yanzu haka a Kano, sun ƙaddamar da cibiyar aikin yin e-Passport da aka inganta na zamani, kuma suna ci gaba da faɗaɗawa zuwa sauran wurare.
Wanda ya wakilce shi a wajen taron, ACG Sadat Hassan, ya ce, ya yi matuƙar farin ciki da jin irin ci gaban da ake samu a dukkan sassan yin fasfo ɗin a dukkan faɗin ƙasar nan, wanda ya nuna yadda mutanenmu ke bayar da cikakken haɗin kai. “Mun shirya za mu shafe mako biyu cif muna yin wannan aikin daga yanzu har zuwa ranar 21 ga wannan watan na Janairu, wanda kuma a wannan lokacin ne za kamala shirin.”

  • Tinubu Ne Kadai Zai Iya Magance Rashin Tsaro Da Tabarbarewar Tattalin Arziki – Buhari 

Ya kuma ƙara da cewa NIS za ta ci gaba da bayar da fasfo ɗin a tsakanin mako uku zuwa mako shida, kana iya tura bayananka, musamman ga mutanen da ba su da matsala wajen tura bayanan ko kuma a rubuta takardar buƙata.Ya ƙara faɗa da babbar murya cewa NIN na daga cikin shika-shikan yin fasfo wanda kuma dole a tabbatar da cewa, bayanan da ke cikinsu ba su saɓa ba.

“Muna ƙara samun ci gaba ne don haka muke kira ga masu neman fasfo ɗin su guji yin bayanan ƙarya su tabbatar sun yi bayanan da kansu kuma sun biya dukkan kuɗaɗen da hannunsu , za su shigar da bayanansu ta hanyar shiga wannan adireshi, passport.immigration.goɓ.ng.Za kuma mu ci gaba da ƙoƙarin kawo ƙarshen dukkan matsalolin da za a ci karo da su.”

Haka kuma ya ce, zai yi amfani da wannan damar wajen gode wa jama’a kan cikakken goyon bayan da suke samu a wajensu. Haka kuma ya nuna cewa, yanzu haka dai NIS ba ta ɗaukar mutane, kuma duk lokacin da za ta ɗauka za ta sanar a kafafe yaɗa labarai, wato lokacin da muka samu amincewar gwamnatin tarayya.

NIS

Shugaban hukumar, Jere ya tabbatar da cewa, jami’an hukumar a tsaye suke ƙyam wajen ganin ganin sun gudanar da ayyukansu kamar yadda doka ta tanada, saboda haka ne ne ma y ace kullun suke ƙara samun ci gaba wajen gudanar da ayyukansu musamman a ɓangaren gudanar da fasfo da ɓangaren tsaro da samun walwala.

Saboda haka ne ma NIS take son isar da saƙonta ga dukkan jama’a cewa akwai fasfo guda 110,000 da masu su ba su zo sun karɓa ba a jihohi 36 da ke ƙasar nan da Abuja. Saboda haka, shugaban hukumar ya raba manyan jami’an hukumar tun daga kan mataimakinsa zuwa shiyya-shiyya domin ganin an tafiyar ta tsarin bayar da fasfo ɗin kamar yadda ya kamata.

Saboda haka ne ma ake shawartar ‘yan Nijeriya waɗanda suka yi fasfo ɗin ba su karɓa ba su je ofishin yin fasfo na NIS ɗin su duba nasu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
An Yi Shawarwari Karo Na 8 Bisa Manyan Tsare-Tsare Tsakanin Sin Da AU

An Yi Shawarwari Karo Na 8 Bisa Manyan Tsare-Tsare Tsakanin Sin Da AU

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version