NNPP Ba Ta Da Kudin Kalubalantar Nasarar Tinubu A Kotu –Buba Galadima
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPP Ba Ta Da Kudin Kalubalantar Nasarar Tinubu A Kotu –Buba Galadima

byAbubakar Abba
2 years ago
NNPP

Jigo a jam’iyyar NNPP Buba Galadima ya bayyana cewa, NNPP taki kalubalantar nasarar da zababben shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya samu a zaben shugaban kasa na 2023 a gaban kotu ne, domin ba ta da kudin da za ta yi hakan.

Galadima ya sanar da hakan ne a hirarsa da gidan talabijin na ARISE a kan ganawar sirri da tsakanin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na NNPP da Tinubu a kasar Faransa.

  • EFCC Na Binciken Gwamnan Zamfara Kan Almundahanar Biliyan 70
  • Xi Da Mai Dakinsa Sun Jagoranci Bikin Maraba Da Baki Mahalarta Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

An ruwaito cewa, Tinubu ya yi ganawar sirrin ne da Kwakwaso don ya samar da masahala a tsakanin Kwankwaso da Abdulmumin Jibrin, tsohon jami’in yakin neman zaben Tinubu kuma zababben dan majalisar wakilai da ya sauya sheka zuwa NNPP daga APC kafin zaben 2023.

Sai dai, ba a samun cikakkun bayanai kan ganawar sirrin da Tinubu ya yi da Kwankwaso ba, amma an ce, sun tattauna kan kafa gwamnatin hadin kan kasa a tsakanin jami’iyyun biyu.

Galadima da yake mayar da martani kan ganawar sirrin ta manayn ‘yan siyasar biyu ya ce, babu wani labari domin abu ne da bisa tahirin siyasar Nijeriya, hakan ya saba farauwa.

Ya ci gaba da cewa, komai yau a Nijeriya ya na zama labarai, inda ya ce, ganawar a tsakanin jagororin ‘yan siyasar biyu, bai kamata ace ta ja hankalin mutane ba.

Ya ci gaba da cewa, kamar yadda ku ka sani ne, Kwankwaso ya yi takarar shugaban kasa da Tinubu a 2023, inda NNPP ta zo na hudu, inda ya sanar da cewa, NNPP ce kawai ba ta je kotu ba, wanda mune ke da cikakkun dalilan zuwa kotu.

A cewarsa, ganawar sirri irin wannan da kuma tunanin kafa gwmnatin hada kan kasa, ba sabon abu ne a harkar siyasar Nijeriya ba domin irin wannan, ta taba faruwa a jamhuriya ta farko a tsakanin jami’yyun NCNC da NPC a taakanin jam’iyyun Azikiwe da Ahmadu Bello.

Ya bayyana cewa, daga baya sun kafa gwmnatin hada kan kasa a tsakanin NPC da NNDP wadda Cif Samuel Akintola na gabas ya jagoranta.

Ya kara da cewa, har ila yau, a rubuce yake a lokacin gwamnatin Shagari, jami’yyar NPP da Nnamdi Azikiwe ke jagoranta, sun kulla yarjejeniya da gwmnatin NPN.

Galadima ya yi nuni da cewa, wannan tarihi ne ya sake mai-maita kansa, a saboda haka ya na da kyau a ilimantar da matasa kan tarihin kasar su.

Da yake mayar da martani kan abinda yasa NNPP ba ta kalubalanci nasarar Tinubu a kotu kamar yadda PDP da LP da sauran jami’iyyu suka yi, ba Galadima ya ce, NNPP ba ta da wadatattun kudin da za ta yi hakan.

Ya ce, wannan abun a rubuce yake cewa, PDP ce ta kore mu ni da Kwankwaso, ba wai mun shiga takarar don mu dakatar da su daga cin nasara a zaben bane.

Ya ce, muna sane da cewa, zuwa kotu na bukatar kudade masu yawa wanda bamu da su, inda ya ce, duk wanda zai je kotu don kalubalantar zabe, akalla sai ya tanadi Naira biliyan biyar, mu kuma, ba mu da wadannan kudaden.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Matsalar Kasa Biyan Basusukan Da Amurka Take Fuskanta Za Ta Kawowa Duniya Asara

Matsalar Kasa Biyan Basusukan Da Amurka Take Fuskanta Za Ta Kawowa Duniya Asara

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version