NNPP Ta Musanta Yarjejeniyar Yi Wa Abduljabbar Yafiya Idan Ta Ci Zaben Gwamna A Kano
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NNPP Ta Musanta Yarjejeniyar Yi Wa Abduljabbar Yafiya Idan Ta Ci Zaben Gwamna A Kano

bySadiq
3 years ago
Abduljabbar

Jam’iyyar NNPP a Jihar Kano ta musanta rade-radin da ake na cewa akwai wata yarjejeniya a kasa da dan takarar gwamnanta na jihar, Abba Kabir Yusuf ya yi na yafe wa Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara idan ya ci zabe.

Wannan dai na kunshe ne cikin wata sanarwa da lauyan dan takarar Barista Abba Hikima, ya fitar a ranar Litinin.

  • INEC Ta Ayyana Shekarau A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaben Sanatan Kano Ta Tsakiya
  • Kwankwaso Ya Lashe Kano, Ya Bai Wa Tinubu Da Atiku Gagarumar Tazara

“Muna son jan hankalin mutane kan wani bidiyo da ake yadawa a kafafen sada zumunta cewar akwai yarjejeniya tsakanin dan takarar gwamnanmu Abba Kabir Yusuf da Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara na ganin an sake shi idan muka ci mulki.

“Dan takararmu ya nesanta kansa da wadannan kalamai inda ya ce babu wata hujja da za ta nuna ya yi wannan alkawari.”

Tun da fari sai an yada wani bidiyo inda ake ikirarin Abba Kabir Yusuf na shirin sakin Abduljabar da zarar ya lashe zaben gwamnan Kano da za a yi a ranar 11 ga watan Maris.

Labarin ya karade kafafen sada zumunta ne bayan da dalibin Abduljabbar, Nasir Almaliky Kabara ya wallafa sakon.

Amma a cikin wani bidiyo da ya sake wallafawa ya bayar da hakuri tare da janye kalamansa da ya yi.

A halin da ake ciki yanzu dai jam’iyyar NNPP ta samu gagarumar nasara a zaben da aka gudanar na shugaban kasa, Sanatoci da na ‘yan majalisar tarayya.

Jam’iyyar ta kashe kananan hukumomi 36 yayin da jam’iyyar APC mai mulki a jihar ta lashe kananan hukumomi takwas.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

October 1, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Next Post
INEC Ta Bayyana Sakamakon Zaben Sanatan Zamfara Ta Tsakiya Bai Kammala Ba

INEC Ta Bayyana Sakamakon Zaben Sanatan Zamfara Ta Tsakiya Bai Kammala Ba

LABARAI MASU NASABA

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version