Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Noma, Ma’adinai Zai Kasance Abin Mayar Da Hankali Ga Gwamnatin Tarayya Don Ci Gaban Arzikin Kasar Najeriya

by Tayo Adelaja
September 12, 2017
in RAHOTANNI
3 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Umar Faruk, Birnin Kebbi

Mukaddashin shugaban kasar, Farfesa Yemi Osinbajo, ya ce ma’adinai da noma, zai kasance  abin mayar da hankali ga Gwamnatin Tarayya don maido da tattalin arziki kasar Najeriya.

samndaads

Osinbajo ya bayyan hakan ne a Argungu lokacin kaddamar da kanfanin shinkafar WACOT na Naira biliyan Goma( N10 biliyan WACOT Rice Mill ) a Argungu da ke Jihar Kebbi.

Ya ce  za a ci gaba da  zuba jari a aikin noma da  ma’adanai da sauran wasu wurare domin samar da kamfanoni masu zaman kansu, da kuma wasu wuraren kasuwan ci,  ya bayyana   yunkuri na Gwamnatin Tarayya kan zuba jari a aikin noma da ma’adanai domin samun kudaden shiga  ga kasa da kuma jahohin kasa nan don ciyar da harakokin kasar a matakin gaba.

Har ila yau Osinbajo  ya yaba wa mutanen da ke zuba jari a cikin kanfanin shinkafa na  WACOT  domin shine zaya kawo ci gaba da bunkasa kanfunnan masu zamankan su  a  shirin bunkasa noman shinkafa  da cashewa, musamman a kan ci gaban mutanen kasar Najeriya.

Ya yi kira ga masu zuba hannun  jari su shiga cikin aikin noma, samar da aikin yi ga marasa aikin yimutanen, musamman idan akai la’akari kan rashin  zuba hannun  jari a masana’atu na Gwamnati da masu zaman kansu,  rashin yin hakan ya haifar da asarar hanyoyin ayyuka a fagen noma da kuma ma’adanai dama sauran masana’atu na kasar nan.

Bagu da kari  Mukaddashin Shugaban kasar ya tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya zata ci gaba da bada  goyon baya ga kamfanoni masu zaman kansu “kasancewa cewa hanya ce ta ci gaba da kuma damar samun aiki yi ga jama’ar kasar Najeriya. ‘’

Hakazalika, ya nemi kanfanin WACOT da su fito da shirin horas da manoma dubu 5,000 domin kara samar da isashiyar  shinkafa a kasar nan.

Shima a nashi  Gwamna Atiku Bagudu ya bayyana cewa  wannan gwamnatin ta karfafa  karuwa  shinkafa maiyawa da amfani a kasar nan daga  ton  biyu a kowace kadada zuwa ton 11  a kowace kadada.

Ya ce wannan  hadin kai tsakanin jihar da kuma kamfanoni masu zaman kansu  da  baban banki Najeriya don bayar da gudummawar  inganta samar da abinci da kuma abinci tsaro.

Har ila yau  ya ce duk da haka, ya bukaci Gwamnatin Tarayya ta ci gaba da bada goyon baya ga kananan da kuma manyan manoma domin karin noma da abinci a kasar nan.

Shima da ya ke gabatar da jawabin sa shugaban zartarwa na  kanfanin  WACOT Mill Nig. Ltd, Mr Rahul Sabara, ya ce kamfanin zai ci gaba da raya aikin horas da manoma dubu dari da ashirin( 120,000)  a kowace shekara. Har ila yau ya ce  zasu samar da aiki ga mutane dubu uku da dari biyar( 3,5000 ) a matsayin ma’aikatan kafanin na WACOT,  yayin da manoma dubu hamsi (50,000) ne zasu ci gajiyar shirin tallafin noma na kanfanin nasu don samar da shinkafa ga kamfanin.

Har ila yau    Ya ce kamfanin fara da daukar ma’aikata dubu daya kuma ‘yan asulin jihar kebbi kafin nan zuwa da wani lokaci. Hakazalika ya kara da cewa kanfanin zaya samar da shinkafa ton 400 a kullum jihar ta kebbi domin samun sauki ga ‘yan kasuwa.

Daga nan ya godewa mukaddashin shugaban kasa daGwamnatin jihar kebbi da kuma jama’ar jihar kan irin gudunmawa da goyun baya da aka ba kanfanin sa domin samun nasarar kaddamar da shi cikin nasara, batare da wata matsaba.

SendShareTweetShare
Previous Post

Kamfanin Oando Ya Samu Ribar Naira Biliyan 4.6

Next Post

Bankin Bunkasa Noma Da Ruwa Zai Kashe Dala Biliyan 400 A Fadin Kasar Nan

RelatedPosts

Makiyaya Ondo

Korar Makiyaya A Ondo: Cikakken Rahoton Yadda Ta Kaya Taron Gwamnoni Da Shugabannin Fulani

by Muhammad
15 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Gwamnonin Nijeriya sun kira taron gaggawa...

Kasafin 2021

Hotunan Sabbin Shugabannin Rundunonin Tsaro

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Major-Gen. Leo Irabor, Chief of Defence...

Garban

Garban Kauye Farawa Ne Allurar Dinke Barakar Kumbotso – Muslihu Yusuf Ali

by Muhammad
3 days ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana zaben Sabon shugaban Karamar...

Next Post

Bankin Bunkasa Noma Da Ruwa Zai Kashe Dala Biliyan 400 A Fadin Kasar Nan

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version