Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home MANYAN LABARAI

Noman Shinkafa: Obasanjo Ya Caccaki Shagari

by Tayo Adelaja
October 28, 2017
in MANYAN LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Sabo Ahmad, Zariya

Tsohon shugaban ƙasa, Chief Olusegun Obasanjo, ya faɗa ranar Alhamis ɗin ta gabata cewa, noman shinkafa ya fara bunƙasa a Nijeriya tun daga shekara ta 1979, lokacin da ya zama shugaban ƙasa ƙarƙashin mulkin soja, kafin lokacin mulkin shugaban ƙasa Alhaji Shehu Shagari, a jamhuriya ta biyu.

samndaads

Obasanjon ya bayyana hakan ne lokacin da yake jawabi a matsayinsa na babban baƙo mai jawabi a wajen ƙaddamar da kamfanin casar shinkafa na Okun Rice, a garin Abeokuta, ta jihar and Ogun.

Obasanjon ya alaƙanta koma-bayan da aka samu a kan harkokin bunƙasa noman shinkafa a ƙasar nan da rashin ɗorewar gwamnati, wanda ya ce, gwamnatin da ta biyo bayan gwamnatinsa ita ce ta Alhaji Shehu Shagari, wadda maimakon ta ƙarfafa tsarin da ya bari na ƙoƙarin bunƙasa noman shinkafar, sai ta naɗa kwamitin da zai dinga shigo wa da ita daga waje. Ya ce, rashin ci gaba da wannan tsarin da ya bari na hanyoyin bunkasa noman shinkafar ya jefa manoma cikin tasku, domin maimakon a sayi shinkafar cikin gida, yadda manomanmu za su samun ƙarfin gwiwar ci gaba da noma ta, sai aka koma sayen shinkafar ƙasar waje.

Obasanjon ya jijina wa shugaban kamfanin casar shinkafar Mista Biodun Onalaja, bisa jajircewar da ya yi wajen ganin wannan aiki ya ci gaba da gudana, wanda yin hakan ba abu ne mai sauƙi ba. Saboda haka, sai ya ƙara da cewa, yana kallon Onalaja a matsayin gwarzo, wanda ya samu nasara a kan harkar bunƙasa noman shinkafa a ƙasar nan. Sannan ya ce, da ƙasar nan za ta samu mutum 100 irin su Onalaja da ta zama mai dogaro da kanta a noman shinkafa, har ma ta zama tana kai wa ƙasashen waje.

A ƙarshe, Obasanjo ya roƙi bankuna da su tallafa wa manoma da bashi, ba tare cajin kuɗin ruwa mai yawa ba, yadda manoman za su iya biyan kuɗin da suka ranta cikin sauƙi.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Dubun Masu Garkuwa Da Mutane Ta Cika A Hanyar Abuja

Next Post

Ya Harbi Mata 30 Da Cutar Ƙanjamau

RelatedPosts

'Yan Adaidaita

An Sasanta Yajin Aikin ’Yan Adaidaita Bayan… Motocin ‘Kano Line’  Sun Koma Jigilar Jakara-Kasuwa

by Muhammad
1 week ago
0

Babu Hanunmu A Ciki Wannan Yaji – Shugaban ’Yan Adaidaita...

Adaidaita

Yajin Aikin Adaidaita: Acaba Ta Dawo A Kano

by Muhammad
1 week ago
0

Ya Jefa Jama’a Cikin Tsaka Mai Wuya Yadda Aka Koma...

Masu Garkuwa

Tattaunawa Da Masu Garkuwa: Yadda Gwamnonin Kaduna Da Neja Suka Raba Gari

by Muhammad
1 week ago
0

Shin Sheikh Gumi Ne Ya Raba Tsakani? Daga Nasir S....

Next Post

Ya Harbi Mata 30 Da Cutar Ƙanjamau

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version