Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home KASUWANCI

Noman Shinkafa Ya Kawo Mana Ribar Naira Biliyan 216 –Bankin Manoma

by Tayo Adelaja
October 30, 2017
in KASUWANCI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abubakar Abba

Bankin Manoma na ƙasa( BOI) ya sanar da cewa Najeriya ta ajiye sama da Dalar Amurka Miliyan 600 dai-dai da Naira Biliyan 216 ba sakamakon haɓɓosan da aka yi wurin noman shinkafa a cikin gida, kuma ba tare da dogaro da Shinkafar da ake shigowa da ita daga ƙasar Thailand da sauran ƙasashe ba. Wannan duk ribar inganta noman shinkafa ta gida ne ƙarƙashin shirin gwamnatin tarayya na noman shinkafa.

samndaads

Babban Daraktan Bankin na sashen mulki da kuɗi, Niyi Akenzua ne ya bayyana hakan lokacin da ya jagoranci tawagar mahukuntan Bankin ziyara fadar gwamnan Jihar Oyo Abiola Ajimobi.

Akenzua  ya ce, ya kamata a jinjina wa ƙasar nan a bisa maida hankali da ta yi wajen faniin mai har da kuma ƙara ƙaimi wajen farfaɗo da harkar aikin noma.

Akenzua ya ce ya zama wajibi a bayyana goyon bayan da jihohi ke bada wa akan shirin na noma shinkafa na gwamnatin trayya, inda yace, sakamakon hakan ya tasmo da ƙasar daga shigo da shinkafa.

Ya shawarci gwamnatin jihar ta Oyo da ta shiga sahun tsarin na noman shinkafa na gwamanatin tarayya, inda ya ce, “mun kuma ƙara faɗaɗa shirin ga masu buƙata.”

Babban Daraktan ya bayyana cewar daga ɗaya zuwa biyu na kamfanoni masu sarrafa shinkafa dake ƙasar Thailand, sun rufe saboda Najeriya ta daina shigo da shinkafarsu.

Acewar shi,“ ada muna kashe Dalar Amurka Biliyan 22 don shigo da shinkafa daga ƙasar waje domin mun yi tunani cewar shigo da shinkafar daga ƙasar waje ba zai yi mana alfanu ba.

A nashi jawabin gwaman ya jinjinawa  minitan Noma da karkara Cif Audu Ogbeh a bisa canjin da ya kawo a fannin aikin noma.

Ajimobi ya ce jihar kamata ya yi ta zama mai samar da abinci da zai wadaci ƙasar nan, inda ya ce inda shugabanin da suka shige sun ɗauki aikin noma da mahimmnaci da tuni an yaƙi yunwa da haɓaka tattalin arzikin ƙasa  da kuma samar da aikin yi musamman ga matasan ƙasar nan.

A ƙarshe ya shawarci sababbin mahukuntan Bankin dasu ci gaba da inganta harkar noma musamman don ƙara farfaɗo da aikin a ƙasar nan.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Yadda Na Kafa Kaina Da Sana’ar Wankin Hula –Muhammad

Next Post

An Shawarci Al’ummar Arewa Kan Sana’ Ga Matasa

RelatedPosts

Sugar

Alakar Dake Tsakanin Sukari Ca Ciwon Suga

by Muhammad
2 months ago
0

Da yawa a yankin kasashen nahiyar Afirka ana ganin sukari...

A Na Cigaba Da Zaman Doya Da Man Ja Tsakanin Majalisa Da Shugaba Trump

Ba Da Mugun Nufi Shugaba Buhari Ya Garkame Iyakoki Ba – Ministar Kudi

by Abdulaziz Kabir Muhammad
1 year ago
0

Ministar kudi da tsaretsare, Uwargida Zainab Ahmed Shamsuna, ta sanar...

Gwamnatin Tarraya Ta Kebe Biliyan N2.6 Don Aikin Tashar Mambilla A 2020

by Abdulaziz Kabir Muhammad
1 year ago
0

Sama da shekaru arba’in da suka shude kenan da bada...

Next Post

An Shawarci Al’ummar Arewa Kan Sana’ Ga Matasa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version