NPA Ta Kaddamar Da Shirin Sayar Wa Matatar Man Dangote Danyen Mai
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NPA Ta Kaddamar Da Shirin Sayar Wa Matatar Man Dangote Danyen Mai

byAbubakar Abba
12 months ago
NPA

Hukumar kula da tashoshin Jiragen Ruwa ta kasa NPA, ta sanar da gudunmawar da za ta bayar wajen wanzar da umarnin gwamnatin tarayya a fanin sanya ido na gudanar da aikace-aikace.

Kazalika, ta bayyana rawar da za ta taka, wajen kara tabbatar da tsaro tare da sauran masu ruwa tsaki, domin a tabbatar samun cin nasara a shirin sayar da danyen mai da sauran dangoginsa, a kan farashin Naira ga matatar mai ta Dangote.

  • GORON JUMA’A
  • Hadarin Kwale-kwale A Kaiama: Gwamnan Jihar Kwara Ya Bayar Da Tallafin Naira Miliyan 100

Ta sanar da hakan ne, a cikin sanarwar da Manajin Darakta na hukumar Dakta Abubakar Dantsoho ya fitar.

Dantsoho ya ce, kwamitin wanda ya kasance a karkashin kulawar hukumar, zai sanya ido wajen ganin cewa, ana sayar da danyen man a kan farashin Naira.

Manajin Daraktan ya bayyana haka ne a jawabinsa a wata ganawa da aka gudanar a jihar Legas, inda ya bayyana jin dadinsa a kan hobbasan da hukumar ke ci gaba da yi don ta sauke nayin da aka dora mata.

Dantsoho ya ci gaba da cewa, aikin ya hada da; wasu wakilai na hukumar, jami’an rundunar sojin ruwa, jami’ai daga kamfanin NNPCL da na kamfanin rukunonin Dangote.

Sauran ya ce, sun hada da; jami’an hukumar tattara haraji na kasa FIRS da na hukumar NMASA da kuma na hukumar NDLEA.

An kuma nada babbar jami’a a sashen ayyuka a hukumar NPA Madam Maureen Ogbonna, a matsayin mai kula da sashen OSS.

Kazalika, jaridar PUNCH ta ruwaito cewa, karamin kwamiti na kula da sayar Danyen man a kan Naira, ya tabbatar cewa, NNPC ya tura danyen man zuwa ga matatar man Dangote, wanda aka sayar wa da kamfanin a kan Naira, a ranar daya ga watan Okutobar 2024.

Bugu da kari, a ranar 13 ga watan Satumbar 2024, kwamitin ya sanar da cewa, a zaman da majalisar zartarwa da shugaba Bola Tinubu ya jagoranta, ta amince da sayar da danyen mai da sauran dangoginsa ga matatun mai na cikin gida Nijeriya, a kan farashin Naira.

Kwamitin ya sanar da cewa, daga ranar daya ga watan Okutobar 2024, NNPC ya fara tura gangunan danyen mai ga matatar mai ta Dangote da suka kai akalla 385,000 a duk rana daya, wadanda kuma za a biya kudinsu, a kan farashin Naira.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

October 3, 2025
Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho
Tattalin Arziki

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

October 3, 2025
Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG
Tattalin Arziki

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

September 27, 2025
Next Post
MDD Ta Zartas Da Kudurin Kafa Yanayi Maras Shinge Ga Masu Bukata Ta Musamman

MDD Ta Zartas Da Kudurin Kafa Yanayi Maras Shinge Ga Masu Bukata Ta Musamman

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version