Rabiu Ali Indabawa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home JAKAR MAGORI

NSCDC Ta Ceto Macen Da ‘Yan Uwanta Su Ka Kulle A Daki Wata Biyar

by Rabiu Ali Indabawa
December 8, 2020
in JAKAR MAGORI
2 min read
NSCDC
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

An yi nasarar ceto wata mata wacce ’yan uwanta su ka kulle ta a wani daki tsawon wata biyar. Matar da aka ceto mai suna Saratu Ayuba tana zaune ne a unguwar Bolari da ke garin Gombe. An rufe matar ne bisa zarginta da ake yi da yin cikin shege tare da haifewa, inda rundunar tsaro ta NSCDC a Jihar Gombe ta ceto ta.

Matar mai shekaru 35 wacce ‘yan uwanta su ke zargi da yin cikin shege, sun kulle ta tsawon fiye da wata biyar. An ceto Saratu Ayuba da ke zama a kwatas din Bolari a birnin Gombe sakamakon wasu bayanai da aka samu daga makwabta, bayan sun gano halin da ta ke ciki na azabtarwa. Wasu yayyenta maza ne su ka rufe ta a daki tsawon sama da watanni biyar, bayan zargin cewa ta yi cikin shege da kuma haifewa, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

samndaads

Shaidu sun bayyana cewa an daure Saratu da mari tare da jaririyar da ta haifa ‘yar watanni biyu a cikin wani daki mara tsafta, a gidansu da ke Bolari.

Saratu, wacce ta tsinci kanta a cikin wani yanayi mara kyan gani ba tare da suturar kirki ba, ta ce shayi da biredi kawai ake bata sau daya a rana tsawon watanni biyar da ta yi a kulle.

Ta ce tsohon mijin nata ya yi mata saki biyu bisa kuskure. Ta kara da cewa tana da ’ya’ya biyu a aurenta na farko; Alkasim mai shekaru 10 da kuma Fatima shekara takwas. Sai dai kuma, yayan Saratu mai suna Muhammad Tajuddin ya ce sun kulle ta ne bayan likitoci sun gano tana da tabin hankali.

SendShareTweetShare
Previous Post

Boko Haram: Alaranmomi Sun Yi Addu’o’i Masu Zafi A Borno

Next Post

Kotu Ta Umarci Sufeton ’Yan Sanda Ya Kawo Mahdi Shehu

RelatedPosts

Huhunta

Kashin Kaza Ya Makale A Huhunta Shekara 14

by Rabiu Ali Indabawa
1 day ago
0

Wata mata ‘yar Kasar Sin mai shekara 22 da haihuwa...

Budurwarsa

Ya Kona Budurwarsa Saboda Ta Yanke Alakarsu

by Rabiu Ali Indabawa
1 day ago
0

Wata yarinya tana cikin halin ha'ula'i na rayuwarta bayan da...

Mari

Ya Kwashe Amaryarsa Da Mari A Taron Bikinsu

by Rabiu Ali Indabawa
1 day ago
0

Wani ango ya mari matar sa a gaban bakin da...

Next Post
Mahdi Shehu

Kotu Ta Umarci Sufeton ’Yan Sanda Ya Kawo Mahdi Shehu

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version