Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

NUJ A Yobe Ta Yi Alkawarin Bai Wa Zababben Gwamnan Jihar Goyon Baya

by
3 years ago
in RAHOTANNI
2 min read
Barazanar
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Fashewar Gas A Kano: Ministar Jinkai Ta Nemi A Dauki Matakan Riga-kafi

Uwar kungiyar manema labarai ta kasa (NUJ) reshen jihar Yobe ta taya zababben gwamnan jihar- Mai Mala Buni, murnar samun nasarar zaben sa a matsayin sabon gwamnan jihar Yobe mai jiran gado, tare da shan alkashin goya wa gwamnatin sa baya domin kai jihar tudun mun tsira; da zaran an rantsar dashi, a ranar 29 ga watan Mayun 2019 mai zuwa.
Sakon taya murnar wanda yake kunshe a cikin takadar sakon da shugaban kungiyar, a jihar Yobe, Kwamared Yusuf Alhaji Isah ga zababben gwamnan, kana wadda aka raba ta ga yan jaridu a Damaturu, babban birnin jihar, a ranar Jumu’ar da ta gabata.
Yayin da ya bayyana cewa, zababben gwamnan, dama can mutum ne mai kyakkyawar alaka kuma abokin huldar yan jaridu a jihar; tun farkon shigar sa a fagen siyasa a jihar Yobe- kimanin shekaru 20 da suka gabata.
Ya ce “a matsayin mu na yan wannan kungiya ta manema labarai (NUJ), mun yi masa kyakkyawar shaidar halayen dattaku, wanda kowanne lokaci ba ya yin nesa da yan jaridu a dukan ayyukan sa. Wanda a kwana a tashi, Allah ya damka masa jagorancin al’ummar jihar Yobe baki daya, wanda a namu bangare zamu tallafa masa wajen samun nasarar yiwa jama’ar wannan jihar ayyukan ci gaba”. Ya bayyana.
Har wala yau kuma, Yusuf Isah ya yi amfani da wannan dama wajen yaba kokarin yan jaridu a jihar wajen bayar da ingantattun rahotani dangane da yadda hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta gudanar manyan zabuka a cikin tsanaki da adalci.
Shugaban kungiyar manema labaran (NUJ) ya bayyana yadda a cikin shekaru 20 tsarin dimukuradiyya ya bunkasa a Nijeriya tare da zaburar da shugabanin da suka yi nasarar dare kujerun da suka yi takara da cewa su tuna girman Allah; su cika alkawuran da suka dauka wa talakawa, a lokutan yakin neman zabe.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

NYSC Ta Tura ‘Yan Yi Wa Kasa Hidima 1,781 Bauchi

Next Post

Kanawa Na Da Hakki A Majalisar Wakilai Ta Tarayya

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

by Ahmed Muhammad Dan'asabe
19 hours ago
0

...

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas A Kano: Ministar Jinkai Ta Nemi A Dauki Matakan Riga-kafi

by
21 hours ago
0

...

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

by CMG Hausa
24 hours ago
0

...

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

by
3 days ago
0

...

Next Post

Kanawa Na Da Hakki A Majalisar Wakilai Ta Tarayya

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: