Okupe Ya Janye A Matsayin Dan Takarar Mataimakin Jam’iyyar Labour Ta Peter Obi
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Okupe Ya Janye A Matsayin Dan Takarar Mataimakin Jam’iyyar Labour Ta Peter Obi

byMuhammad
3 years ago
Okupe

Tsohon babban mataimaki na musamman na tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, Dr Doyin Okupe, a ranar Alhamis, ya janye daga marawa takarar Peter Obi na jam’iyyar Labour baya.

Sakamakon haka, jam’iyyar Labour za ta sanar da sabon abokin takarar shugaban kasa a zaben 2023.

  • Maganar Hadewar Kwankwaso Da Peter Obi Ta Rushe
  • Kwankwaso Ka Da Ka Kuskura Ka Sake Alakantamu Da Peter Obi —Kungiyar IPOB

Dokta Okupe ya bayyana hakan ne ta shafin sa na Twitter da aka tabbatar a ranar Alhamis, inda ya ce ya mika takardar janyewa ga hukumar zabe ta kasa (INEC).

Ya rubuta: “A yammacin yau na mika wa INEC takardar janyewa daga mukamin mataimakin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour.

“Shugaban jam’iyyar na kasa zai sanar da wanda zai maye gurbinsa nan ba da jimawa ba. Ina matukar farin ciki da kasancewa cikin ‘yan gaba wajen samun nasarar jam’iyyar Labour.”

Idan zaku tuna cewa, Peter Obi a ranar 16 ga watan Yuni ya mayarwa INEC fom din takararsa da aka kammala da sunan Dr Okupe a matsayin abokin takararsa.

An yi hakan ne bisa bin dokar zabe ta 2022 da kuma ka’idojin INEC na ranar 17 ga watan Yuni domin mika sunayen ‘yan takara.

Kamar yadda dokar zabe ta tanada, jam’iyyar siyasa ba za ta iya maye gurbin dan takarar da aka tsayar da shi ba sai a lokuta biyu; idan wanda aka zaba ya mutu ko kuma idan wanda aka zaba ya janye daga takarar.

Sai dai kuma dangane da janyewar, wanda aka zaba yana da hurumin rubuta wasika ga jam’iyyar siyasar da ta tsayar da shi, wanda ke nuna cewa ya janye daga takarar, wanda kuma dole ne ya kasance tare da takardar shaidar da dan takarar ya rantse.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Next Post
Adadin Motoci Masu Amfani Da Sabon Makamashi Ya Zarta Miliyan 10 A Sin

Adadin Motoci Masu Amfani Da Sabon Makamashi Ya Zarta Miliyan 10 A Sin

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version