Abba Ibrahim Wada">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home WASANNI

Osimhen Yana Ci Gaba Da Samun Sauki – Gattuso

by Abba Ibrahim Wada
January 16, 2021
in WASANNI
1 min read
Osimhen
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Kociyan kungiyar kwallon kafa ta Napoli, Gannaro Gattuso, ya tabbatar da cewa likitocin kungiyar sun gaya masa cewa dan wasan gaban kungiyar, dan Nigeriya, Bictor Osimhen yana ci gaba da murmurewa daga ciwon da yaji a kafadarsa.

Osimhen dai ya dade yana jinya sakamakon ciwon da yake fama dashi a kafada wanda ya hanashi bugawa kungiyar wasa na watanni kuma a cikin tawagar Nigeriya ya samu raunin a lokacin da yake atisaye da ragowar ‘yan wasan Super Eagles.

Bugu da kari dan wasan ya kamu da cutar Korona a lokacin da yazo gida bikin Kirsimeti da kuma bikin murnar zagayowar haihuwarsa sai Napoli ta tabbatar da cewa za a sake yi wa dan wasan  gwajin cutar Korona saboda har yanzu cutar ba ta rabu da shi ba.

Gwaji ya tabbatar dan wasan mai shekarau 22 ya harbu da cutar cobid 19 ne jim kadan bayan dawowarsa daga Najeriya, inda ya je hutun Kiristimeti kuma tuni aka killace shi kamar yadda dokar hukumar lafiyar kasar ta tanada.

Osimhen ya kebe kansa na tsawon kwanaki 14, amma bayan an sake gwada shi sai aka ga burbushin cutar a tattare da shi wanda yake nuna cewa cutar tana tare dashi har yanzu bugu da kari kuma yana fama da ciwo a kafadarsa.

Tun bayan komawarsa kungiyar ta Napoli daga Lille, Osimhen ya zura kwallaye biyu a raga sannan kuma ya taimaka an zura kwallaye hudu cikin wasanni tara daya bugawa kungiyar a kakar wasa ta bana.

SendShareTweetShare
Previous Post

Muna Ci Gaba Ta Tattaunawa A Kan Makomar Ozil – Arteta

Next Post

Bamu Da Uzuri A Wajen Magoya Baya – Zidane

RelatedPosts

Arteta

Arteta Ya Mayarwa Da Paul Merson Martani

by Abba Ibrahim Wada
2 hours ago
0

Kociyan kungiyar kwallon kafa ta Arsenal, Mikel Arteta, ya mayarwa...

Tuchel

Kowane Wasa A Ingila Mai Wahala Ne –Thomas Tuchel

by Abba Ibrahim Wada
2 hours ago
0

Kociyan kungiyar kwallon kafa ta Chelsea, Thomas Tuchel, ya bayyana...

Alaba

Real Madrid Tana Cigaba Ta Tattaunawa Da Alaba

by Abba Ibrahim Wada
2 hours ago
0

Rahotanni daga kasar Sipaniya sun bayyana cewa kungiyar kwallon kafa...

Next Post
Zidane

Bamu Da Uzuri A Wajen Magoya Baya - Zidane

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version