Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home WASANNI

Ozil Ya Sake Yin Abin Bajinta A Arsenal

by Sulaiman Ibrahim
October 8, 2020
in WASANNI
1 min read
ozil
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Dan kwallon kungiyar kwallon kafa ta Arsenal, Mesut Ozil, ya yi tayin zai biya albashin Jerry Kuy, mai shigar mutum mutumin Gunners da ake kira Gunnersaurus bayan da a ranar Litinin Arsenal ta sanar cewar Kuy wanda shi ne ke shigar mutum mutumin Arsenal shekara 27 yana cikin mutum 55 da aka kora daga aiki a kungiyar.

Arsenal ta fada cewar ya zama wajibi ta rage ma’aikatanta, saboda tabarbarewar tattalin arziki da cutar korona ta haddasa kuma wannan yana daya daga cikin dalilan da suka sanya wannan hukunci ya shafa har Jerry Kuy.

samndaads

‘Yan wasan Arsenal da kociyan kungiyar Mikel Arteta suma sai da suka rage albashi kaso 12.5 cikin 100 a watan Afirilu a lokacin da ake tsakiyar annobar cutar Korona kuma an tsayar da wasanni.

“Na ji bakin ciki da Jerry Kuy, wanda aka fi sani da sunan Gunnersaurus wanda ke kashin bayan kungiyarmu cewar an sallame shi, bayan shekara 27 yana aiki,” in ji Ozil dan kasar Jamus kamar yadda ya wallafa a shafinsa na sada zumunta a Twitter.

Su ma jami’an kungiyar sai da suka zabtare wani kaso na albashinsu zuwa shekara daya saboda sakamakon bullar annobar cutar Korona tun cikin watan Maris ta sa ana buga gasar Premier League ba tare da ‘yan kallo ba.

SendShareTweetShare
Previous Post

Kungiyoyin La Liga Sun Zarce Na Firimiyar Ingila Daraja A Turai

Next Post

Partey Zai Kawo Gagarumin Sauyi A Arsenal, Cewar Michael Essien

RelatedPosts

Arteta

Ya Kamata Mu Dora Daga Nasarar Da Muka Samu Kan Newcastle – Arteta

by Sulaiman Ibrahim
20 hours ago
0

Kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ta karbi bakuncin kungiyar Newcastle...

Kociyan Bilbao

Messi Ya Yi Kuskure A Matsayinsa Na Babba – Kociyan Bilbao

by Sulaiman Ibrahim
21 hours ago
0

Kociyan kungiyar kwallon kafa ta Athletico Bilbao, Marcelino Garcia, ya...

Allison

Klopp Ya Jinjina Wa Allison Bayan Wasan Manchester

by Sulaiman Ibrahim
21 hours ago
0

Mai koyar da ‘yan wasan kungiyar kwallon kafa ta Liberpool,...

Next Post
thomas partey

Partey Zai Kawo Gagarumin Sauyi A Arsenal, Cewar Michael Essien

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version