PDP Ta Lashe Zabukan Cike Gurbi, Tsohon Kakakin Majalisar Bauchi Ya Dawo Majalisa
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Lashe Zabukan Cike Gurbi, Tsohon Kakakin Majalisar Bauchi Ya Dawo Majalisa

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Bauchi

Tsohon Kakakin Majalisar dokokin jihar Bauchi, Abubakar Y. Sulaiman, da tsohon mataimakinsa Umaru Dahiru Jamilu (PDP) sun sake komawa Majalisar dokokin jihar biyo bayan nasarar da suka samu a zaben cike gurbi da ya gudana a ranar Asabar. 

Abubakar ya samu nasara ne kan babban abokin karawarsa na jam’iyyar APC, Khalid Abdulmalik.

  • Zaɓen Cike-gurbi: NNPP Ta Yi Nasarar Lashe Zaɓen Kujeru Biyu Na Majalisar Jiha A Kano
  • Minista Idris Ya Ƙaddamar Da Ƙungiyar Kakakin Labarai 

Da yake sanar da sakamakon zaben, baturen zaben cike gurbin dan Majalisar Ningi, Farfesa Ahmad Abdulhameed ya ce Abubakar Y Sulaiman na PDP ya samu nasara ne da kuri’u 11,785 yayin da abokin nemansa na APC Khalid ya samu kuri’u 10,339.

Kazalika, a mazabar cikin garin Bauchi, Hon. Umaru Dahiru Jamilu na PDP shi ne ya lashe zaben cike gurbin, inda ya samu nasarar kayar da Kwamared Aliyu Ilale na jam’iyyar APC.

Baturen zaben mazabar Bauchi cikin gari, Farfesa Isma’ila Y Shehu ya ce, Umaru Dahiru Jamilu (PDP) ya lashe zaben ne da kuri’u 45,240 yayin da Abdullahi Aliyu (APC) ya samu kuri’u. 41,266.

Umaru Dahiru dai shi ne mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Bauchi kafin kotun daukaka kara ta soke nasarar da ya samu. Da wannan matakin zai sake komawa majalisa a matsayin mamba.

Haka zancen yake a mazabar wajen garin Bauchi wato Zungur/Galambi inda baturen zaben Farfesa Adamu Samaila na jami’ar ATBU ya shelanta Hon. Yusuf Ahmed na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben mazabar da kuri’u 2,233, hakan ya ba shi nasarar kayar da abokin nemansa Ibrahim Isa Yuguda na jam’iyyar APC da ya tashi da kuri’u 1,928.

Bugu da kari, kujerar dan majalisar Madada/Chinade kuwa, Baturen zaben mazabar, Farfesa Ahmed Abdulkadir ya ayyana Ala Nasiru Ahmed na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben da kuri’u 13,920 da ya mangare babban abokin nemansa na APC Dantala Ali mai samun kuri’u 9,710.

Jam’iyyar PDP da ke mulki a jihar ta Bauchi ta lashe dukkanin kujerun ‘yan majalisun da aka gudanar a zaben cike gurbi a mazabar Zungur/Galambi, Ningi, da Madara/Chinade.

Sake zaben na zuwa ne bayan da kotun daukaka kara ta soke nasarar da ‘yan majalisun hudu suka samu a zaben ranar 18 ga watan Maris na 2023. Bayan hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben mazabun, kotun daukaka kara ta umarci INEC ta sake gudanar da zabe a rumfuna 42 da suke gundumomin zabe 16 a cikin kananan hukumomi uku na Ningi, Bauchi da Katagum bayan kalubalantar nasarar su da abokan hamayyarsu suka yi.

Sai dai bayan saken zaben dukkanin wadanda aka yi jayayya a kan kujerun su sun sake dawowa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Zabukan Cike Gurbi: PDP Ta Lashe Kujera 2, APC 1 A Sakkwato

Zabukan Cike Gurbi: PDP Ta Lashe Kujera 2, APC 1 A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version