Philippines Ba Ta Da Imani Ko Kadan
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Philippines Ba Ta Da Imani Ko Kadan

byCGTN Hausa
1 year ago
Philippines

Ministan tsaron kasar Philippines, Gilberto Teodoro ya bayyana a shekaranjiya 27 ga wata cewa, tun da gwamnatin kasar mai ci ta hau karagar mulki a shekara ta 2022, kawo yanzu, ma’aikatar tsaron kasar ba ta da masaniya, kana, ba ta taba cimma wata yarjejeniya da kasar Sin, game da rikicinsu kan tekun kudancin kasar Sin ba. Wannan ya shaida cewa, Philippines ta sake musunta yarjejeniyar da ta cimma da kasar Sin kan batun karamin tsibirin Ren’ai Jiao, baya ga musuntawar da shugaban kasar, Ferdinand Marcos, da mashawarcinsa kan harkokin tsaron kasa, Eduardo Ano suka yi.

Domin tabbatar da halin karko da ake ciki a tekun kudancin kasar Sin, kasashen Sin da Philippines sun rattaba hannu kan wata yarjejeniya dangane da batun karamin tsibirin Ren’ai Jiao, a yayin mulkin gwamnatin Rodrigo Duterte. Bisa yarjejeniyar, Philippines ta alkawarta cewa, ba za ta ci gaba da kaiwa jiragen ruwan sojan da ta jibge a can kayayyakin gine-gine ba. Sai dai kuma bisa ra’ayin nuna jin-kai, kasar Sin ta amince da matakin Philippines na kaiwa sojojin jiragen ruwan kayan rayuwa na wani gajeren lokaci. Tun da gwamnati mai ci ta hau karagar mulki a watan Yunin shekara ta 2022 har zuwa watan Fabrairun shekara ta 2023, hukumomin kasashen Sin da Philippines sun kiyaye wannan yarjejeniya, kaza lika, kasar Sin ta gabatar da bayanai sau da dama da suka shafi yarjejeniyar ga manyan jami’an Philippines.

  • Adadin Sabbin Kamfanonin Kimiyya Da Fasaha Masu Saurin Ci Gaba A Kasar Sin Ya Kai 369
  • Li Qiang Ya Jaddada Muhimmancin Gina Tsarin Samar Da Ababen Hawa Masu Aiki Da Sabbin Makamashi Hade Da Na’urori Masu Basira

Amma manyan jami’an Philippines na gwamnati mai ci sun ce ba su da masaniya ko kadan game da yarjejeniyar da gwamnatin da ta shude ta cimma da kasar Sin, sun sani amma sun take sani. Dalilin gwamnatin Philippines na cin amana gami da kaiwa jiragen ruwan sojan da ta jibge ba bisa doka ba kayayyakin gine-gine shi ne, tana yunkurin samun tallafin kasar Amurka, da neman inganta karfin sojanta na ruwa, da cimma burin mamaye karamin tsibirin Ren’ai Jiao har abada. A don haka, har ta zama wata kafa da Amurka take amfani da ita wajen yin shisshigi cikin harkokin shiyyar.

Wasu matakan da Amurka ta dauka, na tsallake jan layi, da girke makamai masu linzami masu cin matsakaicin zango a Philippines, za su kara ta’azzara halin da ake ciki a yankin. Hakikanin gaskiya, wadannan abubuwan da Philippines ta yi, tamkar kai kanta ne ga hallaka. Kaza lika, musunta yarjejeniyar da ta yi, zai sa kasar ta zama mai aikata laifi, dake musunta tarihi, da cin amana, gami da haifar da rudani ga halin da ake ciki a shiyyar. (Murtala Zhang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Yadda Kasar Sin Ke Samar Da Gudummawa Ga Tabbatar Da Bunkasuwar Duniya Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Yadda Kasar Sin Ke Samar Da Gudummawa Ga Tabbatar Da Bunkasuwar Duniya Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version