Abba Ibrahim Wada">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home WASANNI

Pochettino Ya Kamu Da Cutar Korona

by Abba Ibrahim Wada
January 17, 2021
in WASANNI
2 min read
Pochettino
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Kocin kungiyar kwallon kafa ta Paris St-Germain Mauricio Pochettino ya kamu da cutar korona kuma hakan na nufin ba zai jagoranci fafatawa biyu da kungiyar za ta yi ba a nan gaba kamar yadda kungiyar ta bayyana.

A makon nan ne a karon farko tsohon kocin na Tottenham, mai shekara 48 a duniya, ya lashe kofi a tarihi tun bayan da ya fara aikin horas da kwallon kafa bayan da a ranar Laraba, Paris St Germain ta doke Marseille da ci 2-1 ta lashe Fench Super Cup da ake kira Trophee des Champions.

PGS  ta fafata da kungiyar Angers a ranar Asabar a gasar Ligue 1 sannan za ta kara da kungiyar kwallon kafa ta  Montpellier ranar Juma’a, 22 ga watan Janairu kuma duka an tabbatar da cewa Pochettino ba zai halarci wasanninba.

Sanarwar da kungiyar ta fitar ta ce gwajin da aka yi kan Pochettino ya nuna cewa yana dauke da cutar Cobid-19 saboda haka zai killace kansa na tswon lokacin da likitoci suka bukata kafin a sake gwada shi.

PSG, wadda ta lashe kofi takwas na gasar Ligue 1 a baya, ita ce ta biyu a saman teburin gasar bayan ta fafata a wasanni 19, inda take bayan Lyon da tazarar maki daya kuma nasarar da suka yi a kan Marseille ranar Laraba ita ce karon farko da Pochettino ya lashe kofi a tarihinsa na horar da ‘yan wasan kwallon kafa.

Tsohon dan wasan na Espanyol da Argentina, wanda kuma ya kwashe shekara biyu yana buga wasa a PSG a matsayin dan wasa, ya taba jagorantar kungiyar Espanyol, Southampton ta kuma Totttenham kafin ya maye gurbin Thomas Tuchel a PSG.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Ban Damu Da Jita-Jitar Korata Daga Manchester United Ba, Cewar Solkjaer

Next Post

Yawan ‘Yan Jamhuriyar Afrika Ta Tsakiya Da Ke Gudun Hijira Ya Ninka Cikin Mako Daya

RelatedPosts

Nijeriya

Nijeriya Ta Fara Shirin Buga Wasa Da Kasashen Benin Da Lesotho

by Abba Ibrahim Wada
8 hours ago
0

Hukumar kula da kwallon kafa ta Nijeriya, NFF za ta...

Chelsea

Yadda Aka Fafata Tsakanin Chelsea da Liverpool

by Abba Ibrahim Wada
8 hours ago
0

Kungiyar kwallon kafa ta Chelsea ta ziyarci abokiyar hamayyarta wato...

Ronaldo

Ronaldo Ya Sake Kafa Sabon Tarihi

by Abba Ibrahim Wada
8 hours ago
0

Dan wasan gaba na kungiyar kwallon k ata Juventus, Cristiano...

Next Post
Jamhuriyar Afrika

Yawan ‘Yan Jamhuriyar Afrika Ta Tsakiya Da Ke Gudun Hijira Ya Ninka Cikin Mako Daya

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version