Rage Radadi: Gwamnatin Gombe Ta Amince Da Karin Albashin N10, 000 Ga Kowani Ma’aikaci
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rage Radadi: Gwamnatin Gombe Ta Amince Da Karin Albashin N10, 000 Ga Kowani Ma’aikaci

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Gwamnatin Gombe

Gwamnatin Jihar Gombe ta sanar da yin karin albashin naira dubu goma-goma (N10,000) ga kowani ma’aikacin gwamnati a fadin jihar domin rage radadi da matsatsin cire tallafin Mai.

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida a Gombe ranar Juma’a, mataimain gwamnan jihar, Dakta Manassah Daniel Jatau, ya ce, wannan wani bari ne na cikin matakan da gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ke dauka na rage wa ma’aikata matsatsin tattalin arziki da ake ciki sakamakon cire tallafin na mai.

  • Cire Tallafi: Gwamnan Gombe Ya Raba Kayayyakin Abinci Da Kayan Noma Ga Mutane 450,000

Ya ce, gwamna Inuwa Yahaya ya maida hankali sosai kan tabbatar da walwala da jin dadin ma’aikata tare da al’ummar jihar ta hanyar shirye-shirye masu dama kuma masu fa’ida tun lokacin barkewar annobar Korana.

Ya kara da cewa tun lokacin da aka zare tallafin mai, gwamnatin jihar take ta daukan matakai da bijiro da tsare-tsaren da za su taimaka wa jama’a wajen rage musu kaifin matsatsi da shiga takura a sakamakon hakan.

Ya kara da cewa, daga cikin matakan da gwamnatin ta dauka har da raba tallafin naira dubu talatin-talatin (N30,000) wa mutum 420 000 a sassan jihar.

A fadin nasa, wannan karin albashin dubu 10 zai shafi dukkanin ma’aikatan gwamnati na jiha da na kananan hukumomi kuma zai fara aiki ne daga watan Agustan 2023.

Da aka tambayeshi kan zuwa yaushe ne karin zai tsaya, sai ya ce, “Karin dubu 10 kan albashin ma’aikatan babu ranar tsaida shi a yanzu.”

Mataimakin gwamnan ya jinjina ya gudunmawar da ma’aikatan jihar ke bayarwa, ya misaltasu a matsayin injunan da suke taimaka wa gwamnati wajen tafiyar da shirye-shirye da manufofinta.

Jatau ya kuma roki ma’aikatan jihar da su cigaba da kasancewa masu biyayya wa doka da oda, kuma ya roki wadanda har zuwa yanzu ba su samu tallafi ba da cewa su kara hakuri kaso na zuwa kansu.

“Ina kira ga al’umma musamman wadanda har yanzu ba su samu tallafi ba da su kara hakuri, a bangarenmu za mu cigaba da kawo tsare-tsare da kusan kowa sai ya mora da dan abun da muke da shi a hannu,” ya tabbatar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Next Post
An Kaddamar Da Shirin Baje Kolin Inganta Harkar Noma Da Sana’o’i A Kano

An Kaddamar Da Shirin Baje Kolin Inganta Harkar Noma Da Sana'o’i A Kano

LABARAI MASU NASABA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version