Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home MANYAN LABARAI

RAHOTO: Akwai Kyakkyawar Alaka Tsakanina Da Buhari — Saraki

by Tayo Adelaja
June 8, 2017
in MANYAN LABARAI
4 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Mubarak Umar, Abuja

Shugaban Majalisar Dattawa, Alhaji Abubakar Bukola Saraki ya bayyana cewar dangantakar da ke tsakaninsa da Shugaba Muhammadu Buhari a kullum kara karfi take yi, ba kamar yadda wasu mutane ke kallo akwai sabani tsakanin bangaren Majalisar Zartaswa da na Dokoki ba.

samndaads

Saraki ya fadi hakan yayin wata ziyara da Kungiyar Jama’atu Izalatul Bidi’ah Wa Ikamatus Sunnah (JIBWS) karkashin jagorancin Shugabanta, Sheikh Mohammed Sani Yahaya Jingiri a Majalisa ta kai masa makon da ya gabata.

A wata takardar da ya fitar ta hannun Mataimakinsa na Musamman kan Harkokin Jama’a, Mohammed Isa, Bukola Saraki ya musanta zarge-zargen da ake yi cewar akwai takun saka tsakanin bangaransu na Majalisa a kuma na Zartaswa, inda ya ce duka bangarorin biyu suna aiki kafada da kafada da juna ba tare wata tangarda ba.

“Daga lokacin da muka shigo Majalisa, mun karbi takardun bukatun sahalewa daga Fadar Shugaba Kasa guda 196, ciki mun rattaba hannu a 185, guda 11 kacal muka yi watsi da su. Wannan ya nuna mun bada hadin kai wajen tabbatar da kudurori fiye da kaso 90 cikin 100.

“Na san za ku ci karo da maganganun kala-kala a gidajen rediyo, talabijin da jaridu, amma ina mai tabbatar maku wadannan murahu na gwamnati guda biyu suna aiki tare, fiye da majalisun da aka yi a baya. A watan Janairu, na ziyarce shi (Buhari) a Fadarsa kuma na tabbatar masa a shirye muke don mu ba shi goyon baya wajen yin aiki tare da juna. Mutane suna fadar abin da suka ga dama ne kawai, amma tsakaninmu babu wata matsala.

“Tun da har kun kawo min ziyara, to ga sako zan ba ku, ku sanar da mabiyanku da suke jin wasu maganganu a gidajen rediyo, su sani cewar Shugaban Majalisar Dattawa da sauran Sanatoci ba su da matsala da Fadar Gwamnatin Tarayya, tun bayan rantsar da mu komai tare muke yi, saboda haka akwai kyakkyawar alaka a tsakaninmu.” A cewar Saraki.

Saraki ya ce burin Majalisa Dattawa shi ne tabbatar da tsarin Shugabanci mai cike da adalci ta fuskar ci gaban kasa, tattalin arziki, samar da ayyukan yi da kuma ganin dukkan kudire-kudiren da suke gaban Majalisa an rattaba masu hannu sun zama doka.

Baya ga haka ya ce, batun dokar Daidaita Jinsi wadda yanzu haka take gaban Majalisar, za a tabbatar da cewar ba taba mutuncin kowane addini ba, kasancewar an shirya yin adalci ga dukkan mabiyan addinai a kasar nan.

“Har ila yau, ina son shaida maku cewar batun doka Daidaita Jinsi, duk da ta shafi addinai, muna iya bakin kokarinmu don ganin mun tabbatar da ita matsayin doka ba kuma tare da taba wani bangaren na addini ba.

“Babu wata doka da za ta wulakanta addini, saboda haka dole mu sanya wannan a zukatanmu. Mun tattauna batutuwa da yawa game da hakan, rahoton karshe kawai mu jira wanda za mu yi nazari a kai, domin har yanzu dai tattaunawa muke yi, bukata ce aka gabatar, saboda haka babu batun a yi ta cece-ku-ce da ita da sunan addini. Ina tabbatar maku babu wata matsala.”

“Muna bullo da hanyoyi wadanda za su taimaka mana na ci gaba da kasancewa a matsayin kasa guda daya, shi ya sa muke son bin tsarin daidaito tsakanin addinai domin yin aiki tare da juna babu bambanci.” A cewarsa.

Da yake nasa jawabi, Shugaban JIBWIS, Sheikh Sani Yahya Jingir, ya yabawa Bukola Saraki sakamakon rawar da ya taka wajen kin amincewa da batun ‘yan takara Musulmi daga Jam’iyyar APC a matsayin Shugaban Kasa da Mataimaki a zaben 2015, a cewarsa Nijeriya kasa ce ta kowa da kowa ba ta wani addini ba, saboda haka akwai bukatar samar da daidaito a tsarin shugabanci.

Har ila yau Shehin Malamin ya jinjinawa Majalisa bisa tsayuwar daka da ta yi wajen yin wancakali da batun dokar halatta aure jinsi da kuma hukuncin kisa a laifukun da ba su kai na kisa ba, inda ya ce sam Musulunci ba ya tare da wannan tsari. Ya kuma bukaci Majalisar da ta yi wa kowa adalci a dokar Daidaita Jinsi da ake kokarin kafawa.

Ya kuma yi kira da a samar da daidaito wajen dibar ma’aikata da jami’an gwamnati a mukaman siyasa ta hanyar yin amfani da yawan al’ummar da kowane yanki yake da shi. Sannan ya jaddada bukatar da ke akwai na tabbatar da hadin kai tsakanin bangaren Zartaswa da na Majalisa.

Haka zalika Shehin Malamin ya nemi da Majalisa ta sake duba ga yanayin da ake gudanar da jarrabawa share fagen shiga jami’a (JAMB), domin salon da ake bi yana kawo nakasu matuka ga ci gaba ilmi a kasar nan.

A karshe ya yi addu’ar Allah ya bawa Shugaba Muhammadu Buhari lafiya wanda yanzu haka yake kasar Ingila inda ake duba lafiyarsa.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

RAHOTO: Kotu Ta Kori Karar Da Gwamnatin Jigawa Ta Kai Kwamishinonin Lamido

Next Post

NAZARI: Jaridun Da Ake Bugawa Da Harshen Nijeriya Da Kuma Ci Gaban Kasa

RelatedPosts

Rigakafi

Korona: Jiga-jigan Nijeriya Na Sulale Wa Waje Amsar Rigakafi

by Muhammad
17 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Biyo bayan sake bullar annobar Korona...

Kawuna

Kawuna Ya Turo Ni Kano Don Yin Garkuwa Da Mutane, In Ji Maryam  

by Muhammad
4 days ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Maryam Muhammad, wadda ta shahara wajen...

Beli

Ka Sake Ba Ni Beli – Maina Ga Alkali

by Muhammad
5 days ago
0

Ya Ce, Da Gaske Ba Shi Da Lafiya Daga Khalid...

Next Post

NAZARI: Jaridun Da Ake Bugawa Da Harshen Nijeriya Da Kuma Ci Gaban Kasa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version