Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

RAHOTO: APC Reshen Yobe Ta Dakatar Da Shugaban Hukumar NEMA

by Tayo Adelaja
June 22, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Maitela, Damaturu

 

samndaads

Jam’iyyar APC mai mulki a Jihar Yobe, ta sanar da dakatar da sabon Daraktan Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA), Alhaji Mustapha Yunusa Maihaja daga jam’iyyar baki daya.

Matakin wanda shugabanin jam’iyyar suka bayyana, ya zo bisa kan zargin rashin biyayya da uwar jam’iyyar ke yi masa.

Alhaji Abubakar Bakabe ya bayyana cewa “bisa dokar sashe na 21’D’ da kuma a karamin sashe B cikin baka, na kundin dokokin jam’iyyar APC ya baiwa wannan kwamitin gudanarwa damar daukar mataki ga kowanne dan jam’iyyar wanda ya nuna halin rashin biyayya. Bisa ga wannan, Maihaja ya ci mutuncin wadannan dokoki na APC ta inda ya garzaya kotu tare da yin karar zababben Gwamnan da ya lashe zaben 2015, Alhaji Ibrahim Gaidam kuma ba tare da saurare ko kallon kan shugabanin jam’iyyar da gashi ba; ya yi gaban kan sa.

“Duk da matsayin Alhaji Maihaja na dan takarar kujerar Gwamna a APC, ya garzaya kotu tare da kalubalantar dan takarar da jam’iyya ta tsayar a zaben 2015 wanda ya gudana, yana mai zargin cewa ya sha rantsuwa sau biyu – ta farko bayan rasuwar marigayi Mamman Ali, sannan ga na zaben 2011. Duk da wadannan zarge-zarge nashi biyun, ya sha kasa a kotun daukaka kara da ta koli”. Ta bakin Bakabe.

“Har iala yau, jam’iyya ta gano cewa Maihaja ya yiwa dokokin APC karan -tsaye, Idan an duba sashe na ‘A’ mai karamin sakin – layi na 10. Sashen da ya yiwa kowanne dan jam’iyya kan-da-garkin garzayawa kotu da nufin kalubalantar jam’iyya ko jami’an ta dangane da kowanne abu ta hanyar daukar matakin kashin kai wajen sabawa kudin ba”.  Ya nanata

Abubakar Bakabe ya sake bayyana cewa wannan mataki wanda babban Daraktan NEMA ya dauka ya sa jam’iyyar ta dare gida biyu sannan ya jawo rarrabuwar kai da rashin hadin kai, da rashin ganin kima a cikin jam’iyyar APC a Jihar Yobe.

A sa’ilin nan ne sakataren jam’iyyar APC a Jihar Yobe, Alhaji Abubakar Bakabe ya bayyana cewa “bisa ga wadannan dalilai, jam’iyya ta dakatar da Mustapha Yunusa Maihaja shi sai Illa Masha Allah, tare da bashi shawarar cewa hawainiyar sa ta kiyayi ramar jam’iyyar APC dangane da alakanta kansa da ita wajen bayyana kansa dan jam’iyyar, cikin lamurran sa na yau da kullum”. In ji sanarwar.

Duk kokarin jin ta bakin Alhaji Mustapha Yunusa Maihaja dangane da wannan lamari ya ci tura domin wakilinmu ya buga wayar sa a lokuta daban-daban tana kara amma ba a dauka ba, sannan ya aika sakon kar – ta-kwana shi ma dai shiru har zuwa lokacin hada wannan rahoton.

SendShareTweetShare
Previous Post

RAHOTO: Rundunar ‘Yan Sanda Ta Horas Da Jami’anta Kan Sanin Makama Aiki A Bauchi

Next Post

RAHOTO: ‘Gwamnatin Neja Ta Kashe Fiye Da Milyan 200 Kan Ciyarwa Da Azumi

RelatedPosts

NIS Da NAPTIP Sun Sake Shan Damarar Yaki Da Safarar Dan Adam

NIS Da NAPTIP Sun Sake Shan Damarar Yaki Da Safarar Dan Adam

by Yahuzajere
9 hours ago
0

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS) da...

Sabuwar Cuta Ta Kashe Mutum Hudu A Sokoto

Sabuwar Cuta Ta Kashe Mutum Hudu A Sokoto

by Sulaiman Ibrahim
15 hours ago
0

Gwamna jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal Ya sanar da Mutuwar...

Sakatariyar

Sakatariyar Karamar Hukumar Da Ake Wata Guda Ba A Shige Ta Ba A Kano

by Muhammad
23 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Kananan Hukumomi ne ke zaman gimshikai...

Next Post

RAHOTO: ‘Gwamnatin Neja Ta Kashe Fiye Da Milyan 200 Kan Ciyarwa Da Azumi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version