Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RAHOTANNI

RAHOTO: Barazanar Rashin Aiki Ga Matasa Ta Fi Ta Boko Haram — Kuta

by Tayo Adelaja
June 22, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Awwal Umar, Minna

 

An bayyana sana’ar nika da surhe a matsayin sana’ar da ta samo asali a rayuwar dan Adam, shugaban kungiyar masu sana’ar nika da surhe ta jihar Neja, Alhaji Muhammadu Jibo Kuta ne ya bayyana hakan a lokacin rangadin kafafen yada labarai a Minna fadar Gwamnatin Neja.

Jibo Kuta ya ci gaba da cewar “ganin yadda rashin aikin yi ya zama ruwan dare yanzu haka kungiyarsu ta kuduri aniyar mai da hankali a manyan ayyuka guda uku, koyar da matasa sana’ar nika, ba da dama ga wadanda suka manyanta kuma suke muradin sana’ar ta hangar dora shi a hangar da  zai iya cin moriyar sana’ar, na uku kuma yanzu haka kungiyar ta bada dama ga wanda ke da kudi kuma yana son sanya hannun jari a kungiyar ta yadda kungiyar ce za ta dauki nauyi kula da jarin ta yadda mai dukiyar zai Iya cin moriyar ribarsa da dukiyarsa ke janyowa a karshen kowani wata.

“Yanzu haka idan ka cire wadanda ba su yi karatun ba, da wadanda karatunsu bai yi nisa ba a kowani shekara ana samun matasa dubu saba’in da biyar ne ke kammala karatun jami’a wanda dubu sha biyar ne ke iya samun aiki a hannun Gwamnati da wasu kamfanoni, wannan matsalar na rashin aiki ga matasa ya fi matsalar Boko Haram illa a cikin al’umma. Rashin aiki babban matsala ne a rayuwar matasa da al’ummarmu da cigaban tattalin arzikin kasa”.

Da yake karin haske ga wakilinmu, shugaban kungiyar a Neja ta tsakiya, Malam Usman Yakubu ya ce a yankinsu babban matsalar da suke fuskanta bai wuce matsalar wutan lantarki ba, duk da cewar kusan kashi saba’in da biyar na wutan lantarki daga yankinsu ake tatsarsa. “Zamani yazo da kusan komai ya ta’allaka ne a kan wutan lantarki, dan haka muna kira ga Gwamnatin jiha da kamfanonin da ke Samar da wuta a jihar nan da su inganta shi”.

Shugaban ya ce wannan sana’ar ta samarwa jama’a da dama rufin asiri,  “kungiyar mu tana shiga dan walwale matsalolin da suka shafi wutan lantarki ba Wanda bai fi karfinmu ba kuma ita kanta Gwamnati na karuwa da mu wajen kudin shiga”.

Da yake bayani a madadin kafafen yada labarai, babban darakta a kamfanin buga jaridun Newsline Newspapers da Tauraruwa, Malam Ndama Abubakar, ya ce kungiyar duk da cewar jarirya ce ta zo da manufofi nagartattu da kafafen yada labarai za su yayata shi, musamman rayuwar mutumin da ya bar aiki abu ne mai kyau ya samarwa kansa madogara.

SendShareTweetShare
Previous Post

RAHOTO: Dattawan Ibo Sun Fi Na Arewa Kishi – Yusufu

Next Post

BANGON FARKO

RelatedPosts

Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

by Muhammad
1 day ago
0

Daga Hussaini Yero, Gwamnatin jihar Zamfara ta tabbatar da rahotan...

Mota

Yaki Da ‘Yan Ta’adda: Zulum Ya Ba Sojoji Gudummuwar Mota 12

by Muhammad
1 day ago
0

Sheran jiya Juma’a ce gwamna jihar Borno Babagana Zulum, ya...

Tsangaya

Yadda Aka Fara Karatun Tsangaya A Musulunci Da Lalacewarsa A Kasar Hausa – Gwani Yahuza 

by Muhammad
1 day ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Shugaban hukumar kula da makarantun Al’kur’ani...

Next Post

BANGON FARKO

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version