Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

RAHOTO: Burinmu Majalisa Ta Yi Dokar Tilasta Gwajin Kanjamau Kafin Aure — Dakta Bashir

by Tayo Adelaja
June 8, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Mustapha Ibrahim Tela Kano

Babban Daraktan Hukumar Yaki da Yaduwar Cutar Kanjamau ta Jihar Kano, Dakta Usman Bashir ya ce yanzu haka suna da burin gabatar da kudiri ga Majalisar Dokokin Kano domin ta yi dokar da za ta tilasta wa saurayi da budurwa da sauran baligai yin gwajin cutar kanjamau kafin su yi aure.

samndaads

A cewarsa, yin hakan ne zai tabbatar da ingancin lafiyar ma’auratan tare da dakile yaduwar cutar a tsakanin al’ummar Jihar Kano.

Dakta bashir ya bayyana haka ne a yayin bikin ranar yaki da cutar da kuma kokarin da ake na nemo rigakafin cutar da kuma kokarikn kawar da ita a doran kasa. Ya ce an kai shekara ashirin ana wannan kokari na nemo wannan rigakafin cutar kanjamau a duniya amma har yanzu ba a samu ba, sai dai duk da haka ana ta iya kokari kuma da alamun za a samu nasara. A cewarsa, yanzu haka akwai mutum dubu biyar da ake aikin gwaji da binciken rigakafin a kansu a Afrika ta Kudu.

Haka kuma ya ce in dai aka gwada mutum aka ga yana da ita, ana bashi magani to ba shakka baya iya yada ta, don haka ya shawarci dukkan masu wannan larura da su tabbatar suna aiki da dokoki da ka’idojin da aka sa musu na shan magani.

Dangane da adadin mutanen da suka kamu a jihar kuwa, ya ce “adadin masu dauke da wannan cuta a Najeriya su ne kashi uku cikin dari yayin da Kano take da adadin kashi biyu cikin dari na yawan al’ummarta, wato mutum 280,000, kasancewar jihar tana da adadin mutane sama da miliyan goma”.

Ya kuma ce wannan hukuma na iya kokari na ganin ta wayar da kan mutane ta kafofin yada labarai ta yadda za a kauce wa kamuwa da cutar ta kanjamau.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

RAHOTO: Fastoci Sun Ziyarci Masallaci A Kaduna, Sun Yi Bude Baki Da Musulmai

Next Post

RAHOTO: An Yaba Wa Ganduje Kan Ciyarwar Azumi

RelatedPosts

Garban

Garban Kauye Farawa Ne Allurar Dinke Barakar Kumbotso – Muslihu Yusuf Ali

by Muhammad
1 day ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana zaben Sabon shugaban Karamar...

Harkokin Noma

Sarkin Noma Ya Shawarci Gwamnatin Tarayya Ta Kara Kokari Wajen Gyara Harkokin Noma

by Muhammad
1 day ago
0

Daga Bala Kukkuru, Sarkin Noman Jihar Kano, Alhaji Yusuf Umar...

Kwazon Tambuwal

Hobbasar Kwazon Tambuwal Na Fara Biyan Albashi Daga Haraji A 2023

by Muhammad
2 days ago
0

Daga, Sharfaddeen Sidi Umar, Gwamnatin Jihar Sakkwato a karkashin jagorancin...

Next Post

RAHOTO: An Yaba Wa Ganduje Kan Ciyarwar Azumi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version