Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

RAHOTO: Fastoci Sun Ziyarci Masallaci A Kaduna, Sun Yi Bude Baki Da Musulmai

by Tayo Adelaja
June 8, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abdullahi Usman, Kaduna

A cikin makon da ya gabata ne tawagar Malaman Addinin Kirista, karkashin jagorancin Pasto Yohanna Buru, jagoran Cocin ‘Christ Ebangelical Intercessory Followership Ministry’ da ke Unguwar Sabon Tasha Kaduna suka ziyarci wani Masallaci, inda suka yi bude baki da al’ummar musulmi don kyautata alaka tsakanin mabiya addinan guda biyu.

Wakilinmu ya shaida mana cewa a wannan ziyarar da tawagar Fastocin suka kai masallacin ’Yan Doya da ke babbar kasuwar Kaduna, mabiya addinan guda biyu sun ci abinci tare, wanda kuma dama sun saba kai irin wannan ziyara a duk shekara.

Da yake jawabi bayan kammala bude bakin, jagoran tawagar Fartocin, Fasto Yohanna Buru ya bayyana cewa sun zo masallacin ne don taya al’ummar musulmi murnar fara azumin watan Ramadan, da kuma rokon su da su nunka ibadunsu a wannan wata, musamman salloli da karatun Alkur’ani mai girma. Sannan ya roki matasan musulmin da su mayar da hankali zuwa wajen tafsirin Alkur’ani da ake yi a wannan wata don neman yardar Allah.

Fasto Buru ya ci gaba da cewa, “mu a matsayinmu na shugabannin addinin kirista, duk shekara muna zuwa gidan yari mu fidda ‘yan uwanmu musulmai don su yi azumin wannan wata a gidajensu da iyalansu da abokai kamar sauran musulmai. Sannan muna ziyarar Malamai don yin bude baki tare da su. Sannan mukan halarci tafsiri don mu karu gaba daya.”

Malamin ya ci gaba da cewa, “don haka Muna kiran al’ummar musulmai da su yi wa Nijeriya addu’a da kuma shugaban kasa. Sannan su yi addu’a don samun ci gaba mai amfani a kasar nan. Sannan su yi addu’a don marasa lafiyarmu, Allah ya ba su lafiya, sannan su yi addu’a don ci gaba da dunkulewar kasar nan.”

Ya ce, sun san muhimmancin addu’a da kuma azumi, don haka suka zo don yin roko ga al’ummar musulmai da su ci gaba da yi wa kasar nan addu’a don ci gaba da dunkulewar kasar nan waje guda ba tarwatsewa ba.

Da suke nasu jawaban, Fasto George John, da kuma Rabaran John, duk sun bayyana jin dadinsu ga wannan ziyara da suka kai Masallacin. Sannan suka yi kira ga gwamnatocin jihohi da na tarayya da su mayar da hankali wajen shirya tarukan da za su hada kan mabiya addinai daban-daban a kasar nan. Suka ce yin hakan zai taimaka sosai wajen samar da hanyoyin tattaunawa tsakanin mabiya addinan don samar da zaman lafiya a tsakaninsu.

Da ya ke mayar da jawabi, babban Limamin masallacin, Shaikh Ibrahim Kyauta ya bayyana cewa Allah ne kadai zai saka wa Malaman addinin kiristan da suka kawo masu wannan ziyara har suka yi buda baki tare da su.

Daga nan Shaikh Ibrahim ya yi kira ga jama’a da su yi koyi da halin wadannan shugabanni da suka kawo masu wannan ziyara. Ya ce, yana da kyau a rinka kai irin wannan ziyara a wurin aiki ko a wurin ibada, domin yin hakan zai kara dankon zumunci da kaunar juna.

Daga Malamin ya yi godiya ta musamman ga jagoran wannan tawaga, wanda ya ce wannan ne karo na biyar da suke zuwa suna taya su buda baki a wannan Masallaci.

SendShareTweetShare
Previous Post

APC Ta Samu Karuwa A Kebbi

Next Post

RAHOTO: Burinmu Majalisa Ta Yi Dokar Tilasta Gwajin Kanjamau Kafin Aure — Dakta Bashir

RelatedPosts

Tuhumar Malam Abduljabbar Za A Yi, Ba Mukabala Da Shi Ba– Sheikh Khalil

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

Daga Nasir S. Gwangwazo, Abuja Shugaban Majalisar Malamai na Shiyyar...

ISWAP

Boko Haram Ta Yi Garkuwa Da Ma’aikatan Jinkai Bakwai A Dikwa

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

Daga Muhammad Maitela, Maiduguri A harin bayan nan da mayakan...

Makanike

Shari’ar Gonaki: Kotu Ta Aike Wa Rundunar Soja Da Ma’aikarar Shari’a Sammaci

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

Daga Isa Abdullahi Gidan ‘Bakko, Zariya Kotun daukaka kara dake...

Next Post

RAHOTO: Burinmu Majalisa Ta Yi Dokar Tilasta Gwajin Kanjamau Kafin Aure — Dakta Bashir

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version