Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

RAHOTO: Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Irin Masara Na Zamani Ga Manoma

by Tayo Adelaja
June 8, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Ibrahim Ibrahim, Kaduna

A yunkurin Gwamnatin Jihar Kaduna na ganin ta kyautata ma kananan manoma ta hanyar wadata su da kayan iri na noman zamani, Kwamishinar Ma’aikatar Raya Karkara da Birane ta Jihar Kaduna, Hajiya Balaraba Aliyu Inuwa ta kaddamar da wani shiri na baiwa kananan manoman jihar tallafin irin masara na zamani.

samndaads

Irin wanda a turance ake kira “Bossting maize production through balue-kits, an kaddamar da shi ne a Garin Banki da ke Gundumar Leren Dutse a Karamar Hukumar Kubau da ke Jihar Kaduna.

A yayin da take jawabi a bikin kaddamarwar, Kwamishinan Karkara da Raya Birane, Hajiya Balaraba Aliyu Inuwa, ta bayyana cewa, wannan shiri na hadin gwiwa ne tsakanin Gwamnatin Jihar Kaduna da Kamfanin Bunkasa Noman Masara na Zamani, wanda suka hada hannu domin samarwa kananan manoma da irin masarar da zai bunkasa masarar da suke nomawa da fiye da kashi 80 cikin 100.

A cewar Hajiya Balaraba Aliyu, Gwamnatin Jihar Kaduna a karkashin jagorancin Malam Nasiru El-rufai, ta yi tunanin bullo da wannan shiri ne domin ganin ta sauwake ma kananan manoman Jihar Kaduna da ingantattun irin noma na zamani domin su yi kafada da kafada da sauran takwarorinsu manoma da ke fadin duniya. Wanda a cewar ta, an ware ma wannan shiri kudi har naira miliyan 70 domin ganin wannan shiri ya wadatu ga manoma.

Shi ma a nasa jawabin, Shugaban riko na Karamar Hukumar Kubau, Honarabul Kabir Aliyu, ya bayyana jin dadinsa game da wannan shiri da Gwamnatin Jihar Kaduna ta kirkiro da shi, musamman domin samar wa manoma wata hanya a saukake domin inganta albarkatun abin da suka noma fiye da yadda sukeyi a da.

Shugaban Karamar Hukumar ya roki manoman da za su ci gajiyar wannan shiri, da su tabbatar sun yi amfani da wannan dama da suka samu domin ganin sun wadatar da Jihar Kaduna da abinci.

Wani babban jigo a fannin noma da ke Karamar Hukumar Kubau, Malam Hashimu Garba, ya bayyana wannan shiri na noman zamani a matsayin abin da tuni wasu kasashe suka dade suna cin gajiyarsa. Sannan ya yi godiya ga Gwamnatin Jihar Kaduna musamman a kan yadda ta yi tunanin fara gabatar da wannan shiri a yankinsa na Karamar Hukumar Kubau.

SendShareTweetShare
Previous Post

RAHOTO: An Yaba Wa Ganduje Kan Ciyarwar Azumi

Next Post

Buhari Ya Cika Alkawarin Da Ya Yi Wa Jama’a — Yariman Bomo

RelatedPosts

Alaba

‘Yan Kasuwan Arewa A Legas Mu Hada Kai Don Cigaba – Muhammadu Alaba

by Muhammad
18 hours ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai, Hadin kai shi wani babban al’amari...

Jama'a

Taimaka Wa Jama’a Shi Ne Shugabanci Nagari -Matawalle Alagwadun Legas  

by Muhammad
18 hours ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai,   Matawallen Alagbado, Alhaji Muhammadu ya...

Samarun

Yadda Rasuwar Matashi Ta Jefa Mutane Cikin Alhini A Samarun Zariya

by Muhammad
18 hours ago
0

Daga Idris Umar, A ranar laraba ta wannan makon da...

Next Post

Buhari Ya Cika Alkawarin Da Ya Yi Wa Jama’a — Yariman Bomo

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version