Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home MANYAN LABARAI

RAHOTO: Kotu Ta Kori Karar Da Gwamnatin Jigawa Ta Kai Kwamishinonin Lamido

by Tayo Adelaja
June 8, 2017
in MANYAN LABARAI
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Munkaila T. Abdullah, Dutse

A ranar Litinin din makon da ya gabata ne, Kotun Cif majistare ta biyu da ke zamanta a Dutse ta kori karar da Gwamnatin Jihar Jigawa ta takai tsoffin kwamishinoni uku da suka yi mulki a lokacin tsohuwar Gwamnatin Sule Lamido.

Tsoffin kwamishinonin an gurfanar da su gaban kuliya a watan da ya gabata bisa zargin aikata laifuka hudu wadanda suka hada da almundahana, diban kudaden gwamnati ba bisa ka’ida ba, almubazzaranci da dukiyar al’umma wadda ya sabawa kundi na  97, 312, 123(A) da kuma sashi 287 na dokar jihar ta Jigawa.

Zaman kotun wadda mai sharia Ahmed Lamin ya jagoranta, ya bayyana cewa duk da cewar alkalin alkalai na jihar na da ikon maka duk wani mai laifi gaban kuliya, amma yafi dacewa ya shigar da karar a dunkule ba falle-falle ba.

“Don haka a yunkurin kotu na tabbatar da adalci ga kowanne bangare ba zata amince da cin zarafi ko batanci ga kowa ba”. A cewar hukuncin da aka zartar.

Alkali Lamin, nan take ya bayyana cewa kotu ta kori wannan kara gamida ba da umarnin sakin wadanda ake zargi da su tafiyarsu abinsu.

Bayan yanke wannan hukunci, lauyan masu kara BarristaMusa Muhammed Imam ya bayyana wa kotu kudurinsu na daukaka kara, yadda shi kuma lauyan wadanda ake zargi Barrista Yakubu Ruba suka yi na’am da wannan hukunci.

Tsoffin kwamishinonin dai sun hada da Alhaji Nasiru Umar da Alhaji Salisu Indirawa da kuma  Alhaji Abba Daguro.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

RAHOTO: Jami’an Tsohuwar Gwamnatin Shema Za Su Amayo Naira Bilyan 55

Next Post

RAHOTO: Akwai Kyakkyawar Alaka Tsakanina Da Buhari — Saraki

RelatedPosts

Kabilu

Musabbabin Rikicin Kabilu Uku Da Ya Tayar Da Hankali A Gombe Da Adamawa

by Muhammad
23 hours ago
0

Yadda Rangadin Gwamna Inuwa Ta Kaya A Yankunan Kabilun Daga...

Sufeton

Jan Aikin Da Ke Gaban Sabon Babban Sufeton ‘Yan Sanda

by Muhammad
1 week ago
0

Waiwaye Game Da Manyan Sufetocin Da Aka Taba Nadawa A...

Malaman

Yajin Aiki: Malaman Jami’o’i Sun Ratse, Na Kwalejojin Fasaha Sun Tsunduma  

by Muhammad
1 week ago
0

Malaman jami’o’i a karkashin kungiyarsu ta ASUU sun ratse daga...

Next Post

RAHOTO: Akwai Kyakkyawar Alaka Tsakanina Da Buhari — Saraki

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version