Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

RAHOTO: Magidanta Dubu 41 Za Su Amfana Da Tallafin Irin Shuka A Adamawa

by Tayo Adelaja
June 22, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Shafi’u Saleh, Yola

Kimanin magidanta 41,000 aka bayyana cewa za su amfana da tallafin irin shuka a yankin kananan hukumomi tara da matsalar boko haram ta shafa a Adamawa.

samndaads

Shugaban wata kungiyar habaka harkokin noma da abinci ta kasa (FAO) Ahmadou Diop, ya bayyana haka a yayin kaddamar da rabon irin shukan a garin Fufore, inda ya ce shirin wani mataki ne shawokan matsalolin yunwa da karancin abinci a yankin kananan hukumomin bakwai.

Ya ce kungiyar da hadin gwiwar ma’aikatar noma ta tarayya sun gabatar da wani shirin tantance mutane kimanin miliyan biyar da suka fi fuskantar matsalar yunwa a jihohin Borno, Yobe da Adamawa.

“Gabadaya shirin na shawokan matsalar karancin abinci da abinci mai gina jiki ga al’ummar da abun ya shafa ne, a arewa maso gabas domin bunkasa harkokin noma. Kananan hukumomin da za su amfana sun hada da Fufore, Girei, Gombi, Hong, Madagali, Michika, Mubi ta kudu, Mubi ta arewa da Yola ta kudu”.

Da yake Magana a taron, kwamishinan ma’aikatar noma ta jihar, Ahmad Waziri ya shawarci mutanen da za su amfana da tallafin da suyi amfani da irin hatsin shukin ta yadda ya dace.

Kwamishinan ya bayyana cewa an zabi kaddamar da shirin a garin Fufore ne bisa la’akari da yawan ‘yan gudun hijira da ke zaune a Unguwanni a jihar.

Da yake Magana a madadin mutanen da suka amfana Malam Idris Adamu, ya godewa kungiyar bisa tallafin irin shukin da ta basu, ya kuma yi alkarin za su yi amfani da shi ta yadda ya dace.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

RAHOTO: ‘Gwamnatin Neja Ta Kashe Fiye Da Milyan 200 Kan Ciyarwa Da Azumi

Next Post

RAHOTO: Dattawan Ibo Sun Fi Na Arewa Kishi – Yusufu

RelatedPosts

DATA

Har Yanzu Ana Sayar Da (DATA) Kan Tsohon Farashi Duk Da Ragin Kashi 50

by Sulaiman Ibrahim
23 hours ago
0

Yawancin masu amfani da layin sadarwa sun ce har yanzu...

Farfesa Dadari

Yawan Karbo Bashin Da Gwamnati Ke Yi Bai Da Amfani Ga Kasar Nan -Farfesa Dadari

by Sulaiman Ibrahim
24 hours ago
0

Wani Malami a Jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria, Farfesa...

Gobara Ta Yi Sanadiyyar  Mutuwar Uwa Da ‘Ya’yanta Biyu A Kirfi

Gobara Ta Yi Sanadiyyar  Mutuwar Uwa Da ‘Ya’yanta Biyu A Kirfi

by Sulaiman Ibrahim
24 hours ago
0

Ibtila’in gobara ya ci rayuwar mutum uku daga ciki har...

Next Post

RAHOTO: Dattawan Ibo Sun Fi Na Arewa Kishi – Yusufu

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version