Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

RAHOTO: ‘Sarakuna Su Daina Tunanin Shugabannin Siyasa Sun Fi Su Karfi’

by Tayo Adelaja
July 12, 2017
in RAHOTANNI
3 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Awwal Umar, Minna

Mai martaba Sarkin Kagara, Alhaji Salihu Tanko ya nemi ‘yan siyasa da su daina amfani da matasa wajen tada zaune tsaye a kasar nan, domin matasan su ne shugabannin gobe.

samndaads

Sarkin ya yi wannan kiran ne a fadarsa bayan saukowa daga sallar Idi karama ranar Lahadin makon jiya. Alhaji Salihu Tanko ya ce zaman lafiya shi ne babban jigon cigaba a kasa, saboda kasa ba ta taba samun ci gaba sai kowane bangare na al’umma sun yarda su zauna lafiya da juna.

Da ya juya kan manoma da makiyaya kuwa mai martaba sarkin wanda ya kwashe shekaru talatin da biyar kan karagar mulki a masarautar ya ce, “kasar Kagara kasa ce wadda Allah Ya azurta ta a kan noma da kiwo, don haka ya zama wajibi makiyaya da manoma su fahimci anfanin zaman tare da juna su nemi kowace irin hanya ce da za ta iya samar da zaman lafiya a tsakaninsu, dan haka manoma da makiyayi ‘yan uwan juna ne bai kyautu a bari ana samun ‘yan kananan soki-burutsu na tasowa a tsakaninsu ba, dole su kauda bambance-bambancen da ke tsakaninsu wajen samar da zaman lafiya a tsakaninsu ta haka ne kawai za su iya anfana da muradun gwamnati na dawo da martabar noma da kiwo a kasar nan”.

A wani bangaren kuma, shugaban Karamar Hukumar Rafi kuma shugaban majalisar shugabannin kananan hukumomin Jihar Neja (ALGON), Hon. Muhammad Gambo Bojo a wata ziyara da dagattan kasar Kagara suka kai masa, ya jawo hankalinsu da cewar su Iyayen kasa ne kuma Iyayen al’umma ne ya zama wajibi su tashi tsaye wajen fadawa shugabanni ‘yan siyasa gaskiya a duk lokacin da suka ga ana kokarin kaucewa hanya.

Hon. Bojo ya ce su daina tunanin cewar dokar kasa ta baiwa shugaban karamar hukuma karfi a kansu wajibinsu ne su fito su rika ba da shawarwari ga shugabanni, “da haka ne gwamnati za ta iya samun nasarar isar da muradunta ga al’ummar kasa. Yanzu babban aikin da ke gaban karamar hukuma shi ne kirkiro kasuwanni a inda ake bukatar hakan dan samun hanyoyin karin samun kudin shiga kamar a garin Maikujeri da sauran sassan da suka kamata, saukar da wutan lantarki wanda hakan ne zai iya ba da damar bunkasa kananan kasuwanci a yankunan karkara”.

Ya kuma ce “dangane da tsaro, gwamnatin Jihar Neja ta taka rawar gani kwarai musamman wajen inganta tsaro a yankin, domin ta inganta jami’an tsaro da kayan aiki, kan haka ita kanta karamar hukuma ba ta yi kasa a gwiwa ba ta kara kaimi wajen hada kai da jami’an tsaron soja, ‘yan sanda da ‘yan banga wajen zakolu bata-gari da masu fakewa a cikin al’umma da munanan manufa”. Haka bai samun nasara sai an samar wa al’umma walwala da jin dadi dan karamar hukuma ta kara kaimi wajen samar da abubuwan more rayuwa ga al’ummar yankin wanda hakan zai baiwa kowa damar cin moriyar gwamnati na inganta rayuwar ‘yan kasa na gari.

Dan haka Hon. Gambo Bojo ya jawo hankalin matasa da su daina barin ana anfani da su wajen ruguza rayuwarsu, “duk wanda ya baka makami da nufin yaki da wani lallai ba masoyin ka ba ne, ya zama wajibi matasa su yiwa kansu karatun ta natsu, su dawo da martabarsu ta yadda za su iya zama masu dogaro da kansu wajen kirkiro abubuwan da za su iya moriyarsa da kuma kasa, wanda hakan zai iya zama silar karyewar duk wani mai tunanin bullo da abubuwa da yake tunanin zai iya ruguza su”.

A na shi bangare, Hakimin Kusharki kuma Katukan Kagara, Alhaji Aliyu Muhammad Kusharki ya yabawa gwamnatin Alhaji Abubakar Sadik Sani Bello wajen ceto rayuwar al’umma daga hannu bata gari, Hakimin ya ce yanzu a gundumarsa kawai abin da gwamnatin Neja ta yi abin a yaba ne, “samar da jami’an soja wajen fatattakar bata gari a duk cikin sako da lungu na yankunan karkara abin a yaba ne. Kuma yanzu haka ayyukan raya kasa da gwamnatin Neja ta yi a masarautar Kagara idan ba ta zama ta daya a cikin masarautun Neja to lallai tana kan gaba sosai”. Sai ya nemi duk wani mai rike da sarautar gargajiya da siyasa da su yi mai yiwuwa tare da sanya kishi wajen hada hannu dan kawo abubuwan ci gaba a masarautar Kagara. Inda ya kara da cewa “Lallai samun dattijo mai tsoron Allah a matsayin sarki abin a yaba ne, dan wannan shi ne alamar samun nasara a wannan masarauta”. In ji shi.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Abin Mamaki: Kasashe 10 Da Su Ke Gaba Kan Rashawa Da Cin Hanci, Babu Sunan Nijeriya A Ciki

Next Post

BABBAN LABARI Nijeriya Ta Yi Babban Rashi

RelatedPosts

Ta’aziyar Rasuwar Sam Nda Isaiah

Sam Nda-Isaiah Ya Rasu Lokacin Da Ake Tsananin Bukatar Gudunmawarsa – Jami’ar Jos

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Shugabannin jami’ar Jos sun bayyana rashin jin dadinsu dangane da...

Kasuwar Mile 12

Kwamitin Da Shugaban Kasuwar Mile 12 Ya Nada Na Cigaba Da Jajanta Wa Manoman Arewacin Nijeriya

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Sabon kwamitin da Babban Shugaban kasuwar mile 12 Intanashinal market...

Sojoji Sun Farmaki Mahakar Ma’adanai A Zamfara, Sun Cafke ‘Yan Bindiga 150

Ranar Mazan Jiya: Babu Wani Abin Murna Ga Tabarabrewar Tsaro – Dattawa Ga Buhari

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Dattawan Nijeriya a karkashin inuwar gamayyar kungiyar wato (COPANE), sun...

Next Post

BABBAN LABARI Nijeriya Ta Yi Babban Rashi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version