Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RAHOTANNI

RAHOTO: An Yaba Wa Ganduje Kan Ciyarwar Azumi

by Tayo Adelaja
June 8, 2017
in RAHOTANNI
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Kano

An bayyana ciyarwa a azumin da Gwamnan Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje ke yi da cewa abin a yaba ne kwarai da gaske.

Wannan jawabi ya fito daga bakin shugaban Majalisar Mahaddata Alkur’ani reshen Jihar Kano, Gwani Sunusi Abubakar a lokacin da tawagar manema labarai ta ziyarci tsangayarsa wadda ke cikin cibiyoyin da Gwamnatin Ganduje ke samar da abincin buda baki ga al’umma.

Gwani Sunusi Abubakar ya ci gaba da cewa “mu majalisar Mahaddata Alkur’ani reshen Jihar Kano muna godiya kwarai bisa samar da irin wadanan cibiyoyi da ake samar da abinci domin amfanin masu bukata. Halin da ake ciki ya tsananta kwarai, domin magidanta da yawa ne ke zuwa domin karbar nasu abinci, haka kuma muna aikawa ga tsangayu da kuma masallatai da wuraren zaman jama’a domin sa albarka ga wannan aikin alhairi da Gwamna Ganduje ke aiwatarwa”.

Da aka tambaye shi ko adadin kwano nawa ake dafawa a duk rana? Sai ya amsa da cewa “muna dafa kwano goma zuwa sha biyu a duk rana, bayan kunu, kosai, fanke, dabino har da ruwan sha ake sakawa a duk roba guda. An umarce mu da mu tabbatar da samar da ingantaccen abinci wanda kowa zai iya ci tare da gamsuwa”.

Saboda haka ya bukaci Alarammomi a Jihar Kano da su ci gaba da sa wannan gwamnati cikin addu’o’in a wannan wata mai albarka.

Jama’ar da wakilinu ya samu zantawa da su sun bayyana godiya tare da yabawa da irin abincin da ake dafawa a wannan cibiya, inda suka ce ko shakka babu abincin ya kai duk yadda ake bukata “muna yiwa Gwamna Ganduje addu’ar fatan dorewa da wannan aikin alhairi”.

 

 

 

SendShareTweetShare
Previous Post

RAHOTO: Burinmu Majalisa Ta Yi Dokar Tilasta Gwajin Kanjamau Kafin Aure — Dakta Bashir

Next Post

RAHOTO: Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Irin Masara Na Zamani Ga Manoma

RelatedPosts

Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

by Muhammad
1 day ago
0

Daga Hussaini Yero, Gwamnatin jihar Zamfara ta tabbatar da rahotan...

Mota

Yaki Da ‘Yan Ta’adda: Zulum Ya Ba Sojoji Gudummuwar Mota 12

by Muhammad
1 day ago
0

Sheran jiya Juma’a ce gwamna jihar Borno Babagana Zulum, ya...

Tsangaya

Yadda Aka Fara Karatun Tsangaya A Musulunci Da Lalacewarsa A Kasar Hausa – Gwani Yahuza 

by Muhammad
1 day ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Shugaban hukumar kula da makarantun Al’kur’ani...

Next Post

RAHOTO: Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Irin Masara Na Zamani Ga Manoma

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version