Rahoton INEC Ya Nuna Machina Ne Dan Takarar Sanatan APC A Yobe Ta Arewa
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rahoton INEC Ya Nuna Machina Ne Dan Takarar Sanatan APC A Yobe Ta Arewa

bySadiq
3 years ago
Machina

Wasu takardun Hukumar Zabe ta Kasa (INEC), sun nuna cewa Hon. Bashir Machina ne ya lashe zaben fidda gwani na jam’iyyar APC a mazabar Yobe ta Arewa a Jihar Yobe.

Rahoton tawagar INEC da ta aika don sanya ido kan zaben fidda gwani da Omale Samuel, ya sanya wa hannu mai dauke da kwanan wata 28 ga Mayu, 2022, ya kuma nuna cewa Machina ya samu kuri’a 289 daga cikin kuri’a 300 da wakilan APC suka kada.

  • Kotun Daukaka Kara Ta Yi Watsi Da Karar Buhari Kan Sashe Na 84(12) Na Dokar Zabe
  • Muna Da Hujjojin Magudi A Zaben Fid Da Gwanin PDP Na Kaduna Ta Tsakiya – Lauya

Har ila yau, wani rahoto daga ofishin INEC na jihar Yobe kan yadda aka gudanar da zaben fidda gwani na ‘yan majalisar dattawan Yobe ta Arewa, ya nuna cewa an gudanar da zaben ne a gidan gwamnati da ke Gashua, hedikwatar karamar hukumar Bade ta jihar.

Gundumar ‘C’ ta kunshi kananan hukumomin Bade, Yusufari, Jakusko, Nguru, Karasuwa, da Machina.

Rahoton ya kara da cewa an fara zaben fidda gwanin da misalin karfe 11:30 na safe kamar yadda aka tsara, inda ya kara da cewa jami’an tsaro da jami’an zabe na kananan hukumomin da abin ya shafa duk sun halarta.

“Yayin da za a fara zabukan fidda gwani, dukkan ’yan takara da dukkan jami’an jam’iyyar sun hallara domin sanya ido tare da kuma wakilan jam’iyyar.

“An fara zaben fidda gwani ne da bude addu’o’i daga sakataren kwamitin tsare-tsare Alh. Lawan Modu Sheriff,” in ji rahoton.

Tikitin takarar Sanata na APC a Yobe ta Arewa ya haifar da cece-kuce bayan da wanda ya lashe zaben, Bashir Machina, ya dage cewa ba zai bar takarar ga shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmad Lawan ba, wanda a halin yanzu yake wakiltar kujerar sanatan.

Lawan dai ya tsaya takarar neman tikitin takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC, kuma ya sha kaye a hannun Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a farkon watan Yuni.

Sai dai shugabannin jam’iyyar APC na kasa sun mika sunan Lawan ga INEC domin tantance shi a matsayin dan takarar jam’iyyar a Yobe ta Arewa a zaben 2023, lamarin da ya janyo cece-ku-ce a shafukan sada zumunta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Next Post
Za A Fara Watsa Shirye-shiryen talibijin Da Na Rediyo Na CMG A Hong Kong

Za A Fara Watsa Shirye-shiryen talibijin Da Na Rediyo Na CMG A Hong Kong

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version