Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Ranar Mata Ta Duniya: Aisha Buhari Ta Koka Kan Yawaitar Sace Dalibai Da Mata

by Muhammad
March 9, 2021
in LABARAI
1 min read
Aisha
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Rabiu Ali Indabawa,

Uwargidan Shugaban Nijeriya, Hajiya Aisha Buhari, ta koka kan yadda ake cigaba da sace dalibai, mata da ’yan mata ta hanyar ’yan bindiga da masu tayar da kayar baya, musamman a Arewacin Nijeriya.

Aisha a cikin wata sanarwa a yayin Bikin Ranar Mata Ta Duniya da aka wallafa a shafinta na Tiwita, ta ce, “a matsayina na uwa, Ina nuna bakin ciki da radadin wadanda abin ya shafa da iyalai.

“Ni kuma ban san tasirin da wadannan sace-sacen za su iya yi ba wajen juya akalar nasarorin da muka samu har yanzu, musamman ta fuskar ilimin ’ya’ya mata da kuma auren wuri.”

Ta kuma yi kira ga duk masu ruwa da tsaki da su yi amfani da matakan da suke da shi wajen kawo karshen sace-sacen mutane.

Yayin da take yaba wa kokarin mata da ‘yan mata a yakin da ake yi da annobar cutar Korona, ta lura cewa, wannan annoba ta yi matukar tasiri ga mata, ta hargitsa ilimi, sana’o’i da kuma yawaitar rikice-rikicen cikin gida.

Sai ta bukaci kowa da cewa, bayan yada sakon yarjejeniyar Korona, ya kamata su tuna tare da tallafa wa wadanda cutar ta shafa.

SendShareTweetShare
Previous Post

Hukumar Kwastom Ta Gurfana Gaban Kotu Kan Kisan Matashi A Kebbi

Next Post

CP Alabi Ya Zama Sabon Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Bauchi

RelatedPosts

Malamai

Kungiyar Malamai Ta Tallafa Wa ‘Yan Hijira Sun Shirya Taron Bita Na Ramadan

by Muhammad
8 mins ago
0

Daga Mustapha Ibrahim, Kungiyar Hada Kan zauran Malamai da kungiyar...

Zakzaky

Ramadan: El-Zakzaky Ya Raba Tallafin Abinci Ga Mabukata

by Muhammad
13 mins ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, Shugaban harkar musulunci a Nijeriya (IMN)...

Musulmi

Wajibi Ne Musulmi Su Ajiye Bambancin Akida Dan Hadin Kai Da Samun Zaman Lafiya – Shareef Ishak  

by Muhammad
18 mins ago
0

Daga Muhammad Awwal Umar, An bayyana cewar wajibi ne musulmi...

Next Post
Alabi

CP Alabi Ya Zama Sabon Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Bauchi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version