Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home MANYAN LABARAI

Rashawa: An Yanke Wa Tsohon Darakta Hukuncin Shekara 40 A Gidan Yari

by Tayo Adelaja
October 5, 2017
in MANYAN LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abubakar Abba

Babbar Kotu ta Ƙasa da ke Ibadan cikin Jihar Ondo, ta yanke wa Tsohon Darakatan Cibiyar Binciken Aikin Noma da Horaras wa, Farfesa Benjamen Ogunmodede, hukuncin shekaru 40 a gidan Yari. Kotun ta yanke wa Farfesan Benjamen hukuncin ba tare da bashi zaɓin biyan tara ba.

An gurfanar Farfesan ne, a bisa zargin almubazarancin kuɗaɗen da aka ware don biyan albashin ma’aikata da kuma aiwatar da ayyuka a makarantar.

Su kuma Akawu biyu dake aiki a sashen kuɗi na cibiyar, Zacheus Tejumolada Adenekan Clement, su ma an yanke musu hukuncin shekaru 40 a gidan yari.

Da yake yanke hukunci, alƙalin kotun, Mai Shari’a Ayo Emmanuel, ya yanke musu shekaru hur-huɗu akan kowanne laifi ɗaya, sakamakon amsa laifinsu.

Alƙalin ya ce, Ogunmodede da sauran ana tuhumarsu ne akan karkatar da Naira Miliyan ɗari 177 daga cikin Naira Miliyan 600 da gwamnatin tarayya ta tura wa cibiyar. Naira Miliyan 177 ɗin an ce an kashe su ne ba bisa ƙa’ida ba.

A bayanansu na kariya, waɗanda aka yanke wa hukuncin sun ce, sun kasha kuɗaɗen ne wajen bai wa ‘yan majalisar wakilai na Goro da kuma wasu ma’aikata a Ma’aikatar Kuɗi ta Tarayya, waɗanda suka taimaka wajen ganin an fitar da kuɗin.

Sai dai, Mai Shari’a Emmanuel ya yanke hukuncin cewar, tsohon Darakatan da sauran sun amsa laifukan da ake tuhumarsu.

Lauya mai kare waɗanda ake ƙara, Tunde Olupona, ya ce, za su sake yin nazari akan hukuncin don sanin matakin da za su ɗauka nan gaba.

Shi kuwa Lauyan hukumar EFCC, Nkereuwem Anana, ya yi nuni da cewa, hukuncin wani abu ne da ke nuna ana cin nasara a yaƙin da gwamnatin tarayya take yi da cin hanci da rashawa a ƙasar nan.

SendShareTweetShare
Previous Post

Ƙiris Ya Rage Mu Tarwatsa Ondo Aka Kama Ni –Kwamandan Boko Haram

Next Post

Asibitin Fadar Gwamnati Zai Koma Na Kuɗi

RelatedPosts

Allurar Rigakafin

An Fara Yin Allurar Riga-kafin Korona a Nijeriya

by Muhammad
19 hours ago
0

Yau Ake Sa Ran Buhari Da Osinbajo Za Su Karbi...

'Yan Adaidaita

An Sasanta Yajin Aikin ’Yan Adaidaita Bayan… Motocin ‘Kano Line’  Sun Koma Jigilar Jakara-Kasuwa

by Muhammad
2 weeks ago
0

Babu Hanunmu A Ciki Wannan Yaji – Shugaban ’Yan Adaidaita...

Adaidaita

Yajin Aikin Adaidaita: Acaba Ta Dawo A Kano

by Muhammad
2 weeks ago
0

Ya Jefa Jama’a Cikin Tsaka Mai Wuya Yadda Aka Koma...

Next Post

Asibitin Fadar Gwamnati Zai Koma Na Kuɗi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version