Ahmed Muhammad Dan Asabe">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Rashin Jagoranci Nagari Ne Matsalar Mazabata – Hon Adamu

by Ahmed Muhammad Dan Asabe
July 17, 2020
in LABARAI
2 min read
Rashin Jagoranci Nagari Ne Matsalar Mazabata – Hon Adamu
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

A daidai lokacin da zabukan shugabannin kananan hukumomi da kansiloli a jihar Kogi ke kara karatowa, wani matashin dan siyasa kuma dan takarar kansila mai neman wakiltar mazabar gundumar ‘Ward C’ da ke karamar hukumar Lokoja, karkashin tutar jam’iyyar PDP, Honorabul Umar Abbas Adamu, ya ce rashin jagoranci da kuma shugabanci na gari ne manyan kalubalen da mazabarsa ke fuskanta a ‘yan shekarun nan.
Honorabul Adamu, ya furta hakan ne a yayin da yake zantawa da wakilin jaridar LEADERSHIP A YAU JUMA’A a ranar larabar da ta gabata a garin Lokoja, babban birnin jihar Kogi.
dan takarar wanda ya yi alkawarin gudanar da wakilci na gari idan al’ummar mazabarsa suka zabe shi a matsayin kansila, ya kuma ce akwai ayyukan more rayuwa da daman gaske da jama’ar mazabarsa suke bukata, amma sun rasa saboda rashin wakilci na gari.
Kazalika, matashin dan siyasar ya ce, ya yanke shawarar tsayawa  takarar kansilan ne biyo bayan kiraye-kirayen da matasan gundumar na ‘Ward C’ suka rika yi masa na ya fito don cire masu kitse a wuta, ya na mai jaddada cewa, yana da dukkan sharuddodin da ake bukata na tsayawa takarar.
Honorabul Adamu har ila yau, ya yi bayanin cewa akwai kudurori da kuma shirye-shiryen da ya tsara na inganta rayuwar al’ummar mazabarsa ta gundumar ‘Ward C,’ idan har Allah ya ba shi nasarar lashe zaben.
Ya kuma ce yana da yakinin lashe zaben fitar da gwani da jam’iyyarsa ta PDP za ta gudanar don tsayar da dan takararta na kansila a gundumar ta ‘Ward C.’
dan takarar ya kuma yi kira ga hukumar zabe mai zaman kanta ta jiha (SIEC) da ta gudanar da zabukka masu tsafta da inganci ba tare da nuna son kai ko bambancin jam’iyya ba.
Daga bisani, Honorabul Adamu ya yi kira ga dimbin magoya bayansa da su  fito kwansu da kwarkwata don zabarsa a matsayin kansila.
A watan Satumbar wannan shekara ta 2020 ne dai ake sa ran hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Kogi (SIEC) za ta gudanar da zabukkan shugabannin kananan hukumomi da kansiloli a dukkan yankunan kananan hukumomi 21 da ke fadin jihar ta Kogi.

SendShareTweetShare
Previous Post

Noman Damina: Gwamnatin Kebbi Ta Kaddamar Da Kwamitin Taki

Next Post

Zargin Almundahana: Ina So A Kai Ni Kotu – Mahadi Shehu

RelatedPosts

Za A Kulle Duk Layin Da Ba A Yi Rijistarsa Da Katin Dan Kasa Ba Ranar 9 Ga Fabrairu

Za A Kulle Duk Layin Da Ba A Yi Rijistarsa Da Katin Dan Kasa Ba Ranar 9 Ga Fabrairu

by Ahmed Muhammad Dan Asabe
11 hours ago
0

Gwamnatin Tarayya ta kara wa’adin da aka diba wa ’yan...

Sayar Da Kadarorin Gwamnati Zai Taimaki ‘Yan Nijeriya, Inji Minista

Sayar Da Kadarorin Gwamnati Zai Taimaki ‘Yan Nijeriya, Inji Minista

by Ahmed Muhammad Dan Asabe
12 hours ago
0

Ministar Kudi, Zainab Ahmed, ayau Juma’a, ta ce shirin Gwamnatin...

Zakzaky

Matar Sheikh EL-Zakzaky Ta Kamu Da Korona, In Ji Danta

by Ahmed Muhammad Dan Asabe
16 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Matar Shugaban Kungiyar Musulunci a Nijeriya...

Next Post
Dole Nijeriya Ta Jajirce Kan Yaki Da Rashawa –Mai Shari’a Salami

Zargin Almundahana: Ina So A Kai Ni Kotu - Mahadi Shehu

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version