Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Rashin Jari Da Fili Ne Matsalarmu A Harkar Gwangwan, Cewar Jamilu Abdulkadir

by Muhammad
January 13, 2021
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Gwangwan
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

An bayyana rashin kudi masu gida rana da kuma filin gudanar da harkoki a matsayin manyan matsalolin dake ciwa kungiyar masu harkar Gwangawan tuwo a kwarya.

Daya daga cikin manyan masu ruwa da tsaki a harkar na gwangwan dake Lokoja, babban birnin jihar Kogi, Mallam Jamilu Abdulkadir ne ya bayyana hakan, a yayin da yake zantawa da wakilin jaridar LEADERSHIP Ayau a ranan  lahadi a garin Lokoja.

samndaads

Mallam Jamilu wanda dan asalin jihar Kano ne  yace sana’ar gwangwan, sana’a ce mai albarka amma kuma rashin jari da yan kungiyar ke fuskanta na kokarin gurgunta sana’ar su ta gwangwan.

Kazalika ya kara da cewa rashin filayen gudanar da harkar, shima babban cikas ne ga sana’ar, wanda cewarsa yana samun habbaka ganin cewa matasa da dama sun rungumi harkar na gwangwan don dogaro da kawunanansu.

Ya ce, a yanzu haka yana da yara fiye da Ishirin dake aiki a karkashinsa wadanda, a cewarsa akasarinsu da sana’ar na gwangwan suke daukar dawainiyar kansu da iyalansa.

A kan haka nema mallam Jamilu ya roki gwamnatin jihar Kogi data karamar hukumar Lokoja dasu taimaka wa yayan kungiyar da kudade da kuma filaye domin inganta sana’ar su  ta gwangwan.

Sai dai kuma yayi kira ga mambobin kungiyar ta gwangwan dasu zama tsintsiya madaurinki daya, yana mai cewa sai da hadin kai, za a samu ci gaba.

Har ila yau ya gargadi yan kungiyar dasu guji aikata laifufuka da ka iya bata sunan kungiyar, inda har ma yaja kunnensu da cewa duk dan kungiyar da aka kama da aikata laifi, za a mika shi ga hukuma don hukunta shi dai dai da laifin daya aikata.

Daga nan Mallam Jamilu ya yabawa shugabannin kungiyar na gwangwan a bisa kokarin su na hada yayan kungiyar dake jihar ta Kogi.

SendShareTweetShare
Previous Post

Makaho Ya Sanya Kansa A Makarantar Koyon Tukin Jirgin Sama

Next Post

Sata Ta Saci Sata: Mai Garkuwa Ya Fanshi Kansa Akan Miliyan N1.5

RelatedPosts

Ingantaccen zabe

Aniyar Ganduje Ce Ta Haifar Da Ingantaccen Zabe A Kano – Yusif Ali

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana cewa, kyakkyawar aniyar Gwamna...

Kaduna

Sojoji Sun Yi Wa ‘Yan Bindiga Kwanton Bauna A Kaduna

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Sojojin da ke karkashin ‘Operation Thunder...

Farar Hula

Hankula Sun Tashi A Maiduguri Bayan Babbaka Sojan Da Ya Harbi Farar Hula Hudu

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Mutanen Maiduguri sun shiga tararrabi bayan...

Next Post
Mia Garkuwa

Sata Ta Saci Sata: Mai Garkuwa Ya Fanshi Kansa Akan Miliyan N1.5

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version