Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Rasuwar Shugabannin ’Yan Arewa A Legas Ta Girgiza Mutane – Sarkin Hausawan Ikate

by Muhammad
February 18, 2021
in RAHOTANNI
2 min read
Legas
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Bala Kukkuru,

Sarkin al’ummar Hausawan Ikate Malam Mustafa Musti, kuma shugaban kasuwar sayar da dabbobi dake Karamar Hukumar Aja ta cikin birnin lkko, ya bayyana cewar, rasuwar shuwagabanni al’ummar Arewacin Nijeriya mazauna Legas guda uku a cikin shekara daya kacal ta girgiza ‘yan Arewa A Legas.

samndaads

Sarkin na al’ummar Arewacin Nijeriya mazauna unguwar Ikate dake cikin garin Legas ya yi wannan tsokaci ne a unguwar Aja a lokacin da yake karbar gaisuwa tare da rasuwar marigayi shugaban Barebari na Jihar Legas Alhaji Mustafa Mohammed, wanda Allah ya yi masa rasuwa a sanadiyyar hadarin mota a Meduguri a kan hanyarsa ta zuwa Karamar Hukumar Mafa dake Jihar Barno da fatan Allah ya jikansa da rahama.

Ya cigaba da cewa marigayi sarkin Barebarin mutun wanda ya san ya kamata mai kishin addinin Musulunci da son cigaban al’ummarsa, ya yi gwagwarmaya kwarai da gaske a lokacin rayuwarsa a wajen kare hakkoki tare da mutuncin al ummar Arewacin Nijeriya mazauna Legas, da fatan fatan Allah ya jikansa, ya kara da cewa al’ummar Arewacin Nijeriya mazauna legas sun samu jarabta kwarai da gaske a wajan rasa gwar zayen shugabannin su a Legas.

Sannan kuma ya ba da gudum mawar sa awajan hada kawunan al umma tareda kawo zaman lafiya a Legas da kewayanta baki daya in ji shi da fatan Allah ya kawo masu wadansu shugabannin da za su maye gurbin wadancan shuwagabannin da suka rigamu gidan gaskiya wajan aikata ayyukan alheri.

Sannan kuma ya cigaba da shawartar sarakunan Hausawa mazauna cikin garin Legas da sauran shugabanni da su cigaba da hada kawunan junansu domin samun cigaba da zaman lafiya.

A karshe sarkin na Ikate ya ce yana Isar da sakon godiyarsa ga al ummar Jihar Legas in ji shi musam man kwastomomin shi masu zuwa kasuwar shi domin sayan dabbobi yana yima kowa fatan alheri ya ce kuma ya tanadar masu da manya manyan dabbobi domin biyan bukatun kansu da fatan Allah ya cigaba da zaunar da al’ummar Nijeriya lafiya.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Rikicin Kabilanci: Me Mutanen Nan Suke Nufi Da Kasarmu Ne?

Next Post

Shugaban Tsaro Na Katsina Ya Karrama Malamai Da Limaman Jihar

RelatedPosts

Shata Ya Shaida Ma Ni Zan Dade A Bisa Kan Karagar Mulki – Sarkin Ningi

Shata Ya Shaida Ma Ni Zan Dade A Bisa Kan Karagar Mulki – Sarkin Ningi

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

A ranar Talata 15/2/2021 da ta gabata wakilinmu, Dokta Aliyu...

Matasa Su Dage Da Neman Ilimi Da Koyon Sana’oin Hannu – Dakta Ibrahim Agege 

Matasa Su Dage Da Neman Ilimi Da Koyon Sana’oin Hannu – Dakta Ibrahim Agege 

by Sulaiman Ibrahim
4 days ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai Legas Neman ilmi da koyon sana’oin...

Hajiya Ummi Muhammed Ta Zama Sarauniyar Matan Jihohin Yamma

Hajiya Ummi Muhammed Ta Zama Sarauniyar Matan Jihohin Yamma

by Sulaiman Ibrahim
4 days ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai, Legas Koda- yaushe cancanta da rashinta...

Next Post
Kastina

Shugaban Tsaro Na Katsina Ya Karrama Malamai Da Limaman Jihar

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version