Rayuwar Annabi Muhammadu (SAW) Da Abin Da Ya Ta’allaka Da Aurensa (2)
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rayuwar Annabi Muhammadu (SAW) Da Abin Da Ya Ta’allaka Da Aurensa (2)

byDausayin Musulunci
11 months ago
Annabi

Amma Aure ga wanda Allah ya bashi iko, kuma auren bai tauye masa lokacin Ibada ba, ya tsaya da hakkin auren, to wannan daraja ce, irin wannan darajar ita ce a hakkin Annabinmu (SAW).

Wacce yawan matan ba su shagalantar da shi daga hakkin Ubangijinsa ba, kuma su ma matan ya ba su hakkinsu, kai bari ma, yin auren kara masa yawan ibada ya yi kan ibada. Ya ba da hakkin Allah kuma ya ba da hakkin wadanda Allah ya sa a karkashinsa (Iyalansa) ya tsaya wa hakkokinsu na aure da hakkokinsu na ciyarwa da tufatarwa. Ana cewa, yawan aure yana nuna mutum yana da alheri, in mutum bai da alheri dayar ma ba zai iya tsaya wa hakkokinta na ciyarwa da tufatarwa ba.

  • Falalar Ziyarar Kabarin Annabi SAW (2)
  • Rayuwar Annabi Muhammadu (SAW) Da Abin Da Ya Ta’allaka Da Aurensa (1)

An ruwaito hadisi, Annabi ((SAW)) ya ce “yin aure ba ya daga cikin bukatun duniya ta” ko da cewa aure bukatuwar duniyar wasu ce. Annabi ((SAW)) ya ce: ”Hubbiba ilaiya min dunyakum: An soyar min a cikin duniyarku.” Annabi (SAW) ya yi nuni da cewa, Allah ne ya soyar mai da wasu abu daga duniyar mu, sabida shi komai na shi na Allah ne, ya yi nuni da Abu gida biyu: Turare da Mata.

Manzon Allah (SAW) yana son su don Allah, sabida shi ya soyar masa da su, wannan sabaninmu cewa, muna soyayyar wadannan abubuwan ne don sha’awar duniyarmu, sabida yana sa mu katange idanuwanmu daga matan wasu, ya sa mu kame daga sha’awarmu.

Turare, Annabi (SAW) ya kasance yana son turare sabida haduwa da Mala’iku, babu abin da Annabi ya ki sama da wari, kullun Annabi (SAW) yana haduwa da Mala’iku, a wani Hadisi da Annabi (SAW) ya fada, ya ce, ko nawa mutum ya siya turare bai yi almubazzaranci ba. Bayan fa’idar turare na cewa, sabida Annabi yana haduwa da Mala’iku shi ya sa yake yawan amfani da turare, yana daga cikin amfanin turare, bayan tsarki da saduwa da Ubangiji, yana kara karfin sha’awar aure.

Amma son Manzon Allah (SAW) na hakika, wanda Allah ya kebanci zatinshi da shi, shi ne ganin ikon Ubangijinsa (Hadarar Allah) su Mata da Turare, soyar masa aka yi, da, ko kallo ba su ishe sa ba. Ya fi Annabi Yahya Ma’arifar da ta hana shi aure amma shi Annabi Muhammad (SAW) Hadarar Allah yake kallo da ganawa da shi.

Sabida haka, Manzon Allah (SAW), ya bambance tsakanin wadannan soyayya da halaye guda biyu, da fadinsa “An sanya hasken idanuna a cikin Sallah” za ka ji a hadisi yana cewa Bilalu, kira mana Sallah mu huta, yayin da wasu suke ganin Sallah wahala amma shi Annabi (SAW) a wurinsa Hutu ce, a cikinta yake samun sanyin idanunsa.

Annabi (SAW) ya yi daidai da Annabi Isah da Yahya wajen karewa daga fitinar sha’awar matan, amma Annabi (SAW) ya dara wa Annabi Isah da Yahya wajen cewa shi (Annabi Muhammad) ya yi auren kuma ya tsaya da hakkin Ubangijinsa da hakkin matansa.

Manzon Allah (SAW), shi ne shugaban duk wani namiji, duk wani abu da yake nuna Mazantaka ko namiji ke alfahari da shi, Annabi ya haura kowa: in sadaukanta ce, ya fi kowa, in Kyauta ce, ya fi kowa, in hakuri ne, ya fi kowa, kai ya isa dai a son waye Annabi (SAW), a fadin Ubangiji tabaraka wa ta’ala “Lakad kana lakum rasulullahi uswatun hasanatun liman kana yarjullaha wal yaumal akhir: Lallai ma’aikin Allah ya kasance a cikinku abin koyi…”,  Ma’ana duk duniya kowa ya yi koyi da shi.

Yau in aka ce duk mazauna wannan zawiya su yi koyi da mutum daya, lallai kowa ya san an hada wannan mutumin da aiki, ballantana a ce Unguwa, Jiha ko duk Kasar nan kowa ya yi koyi da shi. Amma Annabi Muhammadu (SAW), Allah cewa duk duniya kowa ya yi koyi da shi.

Larabawa, Turawa, Sinawa da mu bakar fata kowa ya yi koyi da shi. Tun da yawan mata, karfin saduwar aure, abu ne da maza ke alfahari da shi, don haka Annabi (SAW) ya fi kowa don ba za a yi wani namiji ya fi Annabi ba.

Yana daga cikin wasan kakacin da aka ruwaito daga Shehu Ibrahim Inyass cewa, akwai wata daga cikin sahabiyarshi, babba ce ta yi aure da yawa tana neman haihuwa ba ta samu ba sai daga baya, in tana lissafin mazajen da ta aura sai ta zagayo carbi, in ta shiga gaida Shehu sai yace mata, yawwa wacce, zo ki lissafa min mazajen da kika aura, nima in lissafa miki matayen da na aura, mu ga ni da ke waye Kudubin.

Akwai ruwayar ba ni Isra’ila, Annabi Sulaiman Matayensa kusan Dubu ne, Annabi Dauda Daruruwa.

Annabi Muhammad (SAW) yana daga cikin wadanda Allah ya ba su karfi da ikon auren Mata ko nawa ne, ba a masa kaidi ba, kuma kowacce ce ta zo ta ce ya Rasulallahi na ba ka kaina, ya amsa, Allah Ya bashi. An ruwaito Sayyada A’isha tana cewa, Ya Rasulullahi ni dai na ga duk abin da kake so sai Allah ya ba ka, amma yanzu a ce kawai da mace ta ce ta ba ka kanta sai ka amsa, ai lalacin matan ya yi yawa.

Sabida wannan karfi da Allah ya bashi, ya halasta masa adadi na ‘ya’ya mata ya aure su shi kadai ban da sauran Mu’uminai.  Sabida haka, duk zuriyar Annabi (SAW) su ma Allah ya ba su wannan gadon karfin.

Haka kuma duk wani magajin Annabi (SAW) shi ma Allah ya bashi wannan karfin, Duwatsu sun kasa daukar nauyin Alkur’ani amma zuciyar Annabi ta dauka, sai magadansa Mahaddata, su ma za ka same su da irin wannan karfin na sha’awar aure.

Wata rana Annabi (SAW) ya ba wa Sahabinsa, Zubairu bin Awwami jinin da aka yi masa kaho ya je ya zubar inda babu wanda zai gani, sai zubairu ya shanye jinin, bayan dawowarsa, Annabi (SAW) ya ganshi ya ce ina ka zubar? Zubairu ya bayyana cewa ya zuba a cikinshi, Sai (SAW) ya ce masa “wailul laka minan nasi, wa wailul linnasi minka: ka shiga Uku daga Mutane, su ma mutane sun shiga Uku da kai” Ma’ana yanzun duk makiyina in ya gan ka, kanka zai yi sannan kai kuma duk karfina kanka zai yi, sadaukantakata da damkata, kanka za ta yi.

A kowacce al’ada, mazaje, alfahari suke da auratayya da mazakantaka wajen iyali, sabida haka, wannan abun yabo ne ba zargi ba.

An ruwaito Hadisi daga dan dakin Annabi (SAW), Anas dan Malik, cewa shi manzon Allah (SAW) in ji Anas Ya kasance yana kewaya dakunan matansa a wani lokaci na dare, amma waninsa ba a yarda ba, dole a bai wa ‘ya kwananta. Matan Annabi a wannan lokacin su goma sha daya ne (11) amma mu karshen matan mu hudu (4), duk da cewa, akwai abubuwan da suke kan (SAW) wanda ya zama dole a kansa mu kuma sabanin hakan, kamar kwana ana Sallah, dole ne a kan (SAW) amma mu ba dole ne ba.

Sahabi Anas, ya ce, mun kasance wata rana muna hira, muna cewa shi (Annabi (SAW)) an bashi karfin namiji 30, ma’ana zai iya saduwa da mace 30 a dare daya. Nasa’i ne ya rahoto wannan Hadisin. An sake ruwaito irinsa daga Abi Ra’fi’in (bawan Annabi ne), an karba daga dawusu (almajirin Abdullahi bin Abbas) shi kuma ya ce, an bai wa Annabi (SAW), karfin namiji 40 cikin saduwa da iyali.

An karbo irin wannan hadisin daga Safwan, Salma (baiwar Annabi ce kila kuma baiwar Safiyyatu ce, ungwazomar sayyada Fatima) ta ce, wata rana Annabi (SAW) a dare daya, ya taba kewaye Matansa Tara a wannan lokaci su Tara ne, amma yana yin wankan tsarki kafin yaje wajen ta gaba.

Malamai sun yi sabani cikin adadin yawan Matan Manzon Allah (SAW), amma dukkansu sun tafi, Matan Manzon Allah (SAW) su 11 ne.

Za mu tashi a kan wannan darasi mako mai zuwa in sha Allahu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taba Yi
Dausayin Musulunci

Annabi (SAW) Shi Ne Mai Girman Duk Wani Mai Girma Da Allah Ya Taba Yi

October 3, 2025
Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (3)
Dausayin Musulunci

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (3)

September 26, 2025
Manzon Allah
Dausayin Musulunci

Muna Murna Da Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (1)

September 5, 2025
Next Post
Ƙone-ƙonen Da Ƴan Ta’adda Ke Yi Zai Ƙara Haifar Da Ƙarancin Abinci

Ƙone-ƙonen Da Ƴan Ta’adda Ke Yi Zai Ƙara Haifar Da Ƙarancin Abinci

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version