Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home MANYAN LABARAI

Rediyon Biyafara: Laifin Nijeriya Ne, Cewar Ingila

by Tayo Adelaja
September 24, 2017
in MANYAN LABARAI
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Nasir S. Gwangwazo,  Abuja

Kasar Birtaniya ta dora alhakin cigaba da watsa labarai da gidan rediyon Biyafara ke yi a Ingila kan gwamnatin tarayyar Nijeriya. Wannan martani ya biyo bayan zargin da ministan yada labaran Nijeriya, Mista Lai Mohammed, ya yiwa kasar ta Birtaniya a makon jiya ne da cewa su ne su ka daure gindin cigaba da wanzuwar haramtaccen gidan rediyon.

Gidan rediyon, wanda mallakar kungiyar fafatukar samun ’yancin kan Biyafara ta MASSOB ce, ya yi kaurin sun a wajen yada kalaman nuna kiyayya ga kasancewar Nijeriya a matsayi kasa daya al’umma daya.

Jagoran fafutukar neman ’yancin, Nnamdi Kanu, mai lasisin zama dan kasar ta Ingila kuma darakta ne a kamfanin, wanda daga bisani ya amshi ragamar gidan rediyon bakidaya. Lai ya yi zargin cewa, Birtaniya ta yi sakacin gaske wajen barin gidan rediyon ya cigaba da gudanar da ayyukansa a kasarta, duk da cewa ya na yada bayanan nuna kiyayya da rashin zaman lafiya da kuma tunzura jama’a ne.

A sanarwar da ofishin jakadancin Ingilar a Nijeriya ya bayar a Abuja karshen makon nan mai dauke da sa hannun jami’in hulda da ’yan jarida na ofishin, Mr. Joe Abuku, a fusace, ya ce, “Birtaniya ba ta da wata masaniya kan ko Nijeriya ta turo da wakilai kan batun Rediyo Biyafara ba.

“Idan da a ce mun samu wani sako kan bukatar hakan, lallai da za mu duba batun gwargwadon irin shaidun da a ka gabato da su bisa la’akari da cewa, ’yancin fadar albarkacin baki ya na da iyaka.”

 

SendShareTweetShare
Previous Post

SIRRINSU Mulkin Mallaka: Yari Ya Mayar Da Zamfara Gidan Yari

Next Post

Bambanci Tsakanin Asibitocin Tarayya Da Na Jihohi: Gwamnatin Sakkwato Ta Sami Mafita

RelatedPosts

Sufeton

Jan Aikin Da Ke Gaban Sabon Babban Sufeton ‘Yan Sanda

by Muhammad
6 days ago
0

Waiwaye Game Da Manyan Sufetocin Da Aka Taba Nadawa A...

Malaman

Yajin Aiki: Malaman Jami’o’i Sun Ratse, Na Kwalejojin Fasaha Sun Tsunduma  

by Muhammad
6 days ago
0

Malaman jami’o’i a karkashin kungiyarsu ta ASUU sun ratse daga...

Gada

Gina Gadojin Sama: Ko Gasa Gwamnonin Jihohin Arewa Ke Yi?  

by Muhammad
1 week ago
0

Ra’ayoyin Kanawa Game Da Gadar Buhari Me Ya Sa Tambuwal...

Next Post

Bambanci Tsakanin Asibitocin Tarayya Da Na Jihohi: Gwamnatin Sakkwato Ta Sami Mafita

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version