Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home NOMA

Rikicin Makiyaya Da Manoma: Rungumar Tsarin Gwamnatin Ganduje Ne Mafita – Masana

by Sulaiman Ibrahim
March 31, 2021
in NOMA
3 min read
Kananan Hukumomin Jihar Kano
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abubakar Abba

Wasu masana a fanni aikin noma sun yi nuni da cewa, akwai matukar bukatar a yi koyi da Dabarun Gwamnan jihar Kano Dakta Abudullahi Umar Ganduje domin magance rikici a tsakanin Fulani Makiya da Manoma a kasar nan.
daya daga cikin masanan kuma Shugaban yankin Igana Olayiwola Adeleke ya nuna gamsuwar sa kan salon fa gwamnatin Ganguje ta Yi amfani dashi wajen rage rikici a tsakanin Fulani Makiya da Manoma a jihar Kano.
Don a kawo karshen mastalar, masanan sun yi kira da samar da ingantattun dabarun tsaro da kuma ci gaba da sa ido domin a magance matsalar baki daya a kasar.
An dai ta faman yin kira ga mahikuntan dake a kasar nan, kan a tabbatar da an kama dukkan Fulani Makiya da suka yi kutse a gonakan manoman dake kasar nan domin a hukunta su kamar yadda doka ta tanadar.
Masanan sun kuma danganta kan yadda iyakokin kasar nan suke a sakakai ne ke janyo Fulani Makiya bakin haure ke shigo wa cikin kasar nan domin yin kiwo.
Misali, a cewar masanan, a yankin Kudu maso gabas, an kafa dokokin da suka haramta wa Fulani Makiya yin kiwo a gurare barkatai, musamman a tsakanin ‘ya’yan Fulani Makiya yara da sauransu, musamman bayan aukuwar tashin tashina a yankin Igangan da kuma a Sasa dake a cikin jihar Oyo.
Har ila yau, gwamnonin Areeacin kasar nan, sun fito da shirin yin kiwo na Ruga, kamar irin wanda Gwamman jihar Kano Dakta Ganduje ya gudanar a jihar.
A dukkan wadannan jihohin na Areeacin Nijeriya, anja kunnen Fulanin Makiyaya da su su tabbatar sun gudanar da ayyukansu na yin kiwo bisa yadda dokokin jihohin suka gindaya..
Bugu da kari, Nijeriya na iya yin kiwo da tsarin kiwo irin na kasar Tanzaniya inda gwamnatin kasar ke ci gaba da yin kokari wajen dakile rikici a tsakanin Fulani Miakiyaya da Manoman kasar ta hanyar samar da guraren yin kiwo ga Fulani Makiyaya.
Har ila yau, Gwamnan na jihar Kano Abdullahi Ganduje, ya shelanta cewa, gwamnatinsa ta yi namijin kokari wajen rage barayin Shanu, inda ta wanzar da shirin Ruga a jihar.
A cewar Gwamnan na jihar Kano a yankin Samsosua dake da iyaka da Jihar Katsina, kuma mun ci nasara wajen rage ayyukan barayin shanu a yankin.
Gwamnan na jihar Kano Abdullahi Ganduje ya ci gaba da cewa, “ Za mu kuma samar da wasu guraren domin gighina Dam-Dam da Fulani makiyaya za su dinga shayar da dabbobin su”.
A cewar Gwamnan na jihar Kano Abdullahi Ganduje, “Mun kuma kafa asibitin kula da lafiyar dabbobi inda tuni, muka fara gina gidajen Fulani Makiyaya ”.
A cewar Gwamnan na jihar Kano Abdullahi Ganduje ya zama wajibi a kirkiro da dokokin yin kiwo domin a dakile matsalar, inda ya yi nuni da cewa, in kuma ba a yi hakan ba, za a cikin gaba kasa kawo karshen matsalar a kasar nan.
Shi ma mataimakin Gwamnan jihar Biniwe Benson Abounu ya yi nuni da cewa, akwai bukatar a kwaikwayi dabarun Ganduje na kafa Ruga, musamman domin a rage rikicin dake aukuwar a tsakanin Fulani Miakiyaya da Manoman kasar nan.
Ganduje, wanda ya kasance a baya, Makiyayi ne, ya na sane da mafita da ya kamata a dauka domin a kawo karshen matsalar.
A cewar bayanan da kungiyar kasa da kasa ta cording dak bibiyar rikice-rikice a tsakanin alumma (ICG), ta sanar da cewa, yawan rikici a tsakanin Fulani Makiyaya da alumomi ya rubanya hare-haren da ‘yan ta’addar Boko Haram har sau shida domin rikicin na Fulani Makiyaya na aukuwa ne kai tsaye, a tsanakin alumma, inda hakan, ya fi shafar farar hula.
Daga shekarar 2010 zuwa shekarar 2015, an samu rikicin Fulani da Makiyaya guda 850 a yankin Middle Belt, inda kuma aka samu mace-macen mutane guda 6,500 aka kuma raba mutane guda 62,000 daga muhallansu.
A shekarar 2016 kadai, ICG ta tattaro bayanai na mace-macen da ya kai 2,500 a tsakanin Fulani Miakiyaya da Manoma, inda wadanda abin ya fi shafa, sun fito ne daga Jihohin Binuwe da Kaduna sai kuma sauran, daga kudancin kasar nan.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Sakon Da Na Aika Cikin Wakar Mai Hakuri – Sadeek Zazzabi

Next Post

Bai Kamata Gwamnatin Tarayya Ta Rika Tilasta Wa Matasa Rungumar Noma Ba, Cewar Kwararre

RelatedPosts

Karo

Nijeriya Da Sudan Da Chadi Suka Fi Fitar Da Karo Zuwa Ketare, Cewar Rahoton UNCTAD

by Muhammad
4 days ago
0

Daga Abubakar Abba, An bayyana cewa Kasashen Sudan da Chadi...

Abinci

Legas Ba Za Ta Ci  Gaba Da Dogaro Da Arewa Wajen Samun Abinci Ba – Gwamnatin Jihar

by Muhammad
4 days ago
0

Daga Abubakar Abba, Gwamnatin jihar Legas ta shelanta cewa tana...

Noma

Abin Da Sabon Binciken Bunkasa Noma Ya Gano A Nijeriya  

by Muhammad
6 days ago
0

Daga Abubakar Abba, Sakamakon wani sabon bincike da aka gudanar...

Next Post
Manoman Alkama

Bai Kamata Gwamnatin Tarayya Ta Rika Tilasta Wa Matasa Rungumar Noma Ba, Cewar Kwararre

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version